HausaTv:
2025-03-06@03:21:51 GMT

Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ta Amince Da Gazawarta Wajen Hana Harin Hamas

Published: 5th, March 2025 GMT

Hukumar leken asiri ta gwamnatin Isra’ila (Shin Bet) ta amince da gazawarta wajen hana harin ba-zata da kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, 2023.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Talata, shugaban hukumar ta Shin Bet, Ronen Bar, ya amince da cewa, hukumar ta ” gaza a cikin aikinta” na dakile ayyukan Operation Al-Aqsa, tare da kutsawa manyan sansanonin Isra’ila bayan da sojoji da ‘yan sandan gwamnatin suka yi kaca-kaca da su.

Ya ce, da hukumar ta Shin Bet ta yi wani abu daban a cikin shekarun da suka gabata kafin harin da kuma a daren da aka kai harin… da an kaucewa hakan.

“A matsayina na shugaban hukumar, zan dauki wannan nauyi a wuyana har karshen rayuwata,” in ji shi.

Hukumar ta amince da gagarumin gibi a cikin tattara bayanan sirri da kuma dogaro da matakan kariya da ake da su, wanda ya haifar da rashin fahimtar kungiyar Hamas, tare da sauran kungiyoyin gwagwarmaya.

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wani “binciken cikin gida” ya nuna cewa, an gaza wajen dakile harin na Hamas.

Binciken da sojojin Isra’ila suka gudanar ya soki yadda gwamnatin kasar ke dogaro da bayanan sirri da kuma raina karfin Hamas, kura-kuran da suka haifar da mummunan sakamako ga gwamnatin Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Ficen Nijeriya — ’Yan sanda

Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta sanar da cewa a ɗakin wani otel ta gano gawar wani tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Ficen Nijeriya, David Shikfu Parradang.

A baya dai an ruwaito cewa wasu masu garkuwa da mutane ne suka kashe Mista Parradang bayan sun karɓe kuɗin da ya ciro a banki a yankin Area 1 da ke babban birnin ƙasar.

Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya

Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Abuja, Josephine Adeh ta fitar a yammacin wannan Talatar, ta ce tsohon babban jami’in Hukumar Shige da Ficen ya mutu ne a ɗakin wani otel saɓanin rahoton da ke cewa masu garkuwa da mutane ne suka kashe shi.

Adeh ta ce rasuwar Mista Parradang na zuwa ne bayan ya yi wata baƙuwa mace da ta kai masa ziyara ɗakin otel ɗin ya kama na kwana guda.

“Bisa rahotanni da ke cewa an yi garkuwa da tsohon jami’in Hukumar Shige da Ficen sannan daga bisani aka kashe, muna so mu tabbatar da gaskiyar lamarin.

“Abin da ya faru shi ne da misalin ƙarfe 12 na ranar 3 ga watan Maris, Mista Parradang ya ziyarci Otel ɗin Joy House da ke yankin Area 3 na Abuja a wata baƙar mota ƙirar marsandi.

“Ya biya Naira 22,000 kuɗin kwana ɗaya. Sai dai bayan wani ɗan lokaci ya buƙaci ɗaya daga cikin masu aiki a otel ɗin cewa ya yi baƙuwa yana so a rako ta ɗakin nasa.

“Matar da ta kai masa ziyara ta bar otel ɗin da misalin ƙarfe 4 na yammacin wannan rana.

“Har bayan tafiyar wannan mata Mista Parradang bai fito daga ɗakin ba, sai washegari da misalin ƙarfe 4 na asubahi wani abokinsa mai aikin ɗamara ya biyo sawu yana cigiyarsa har otel ɗin.

“Yana zuwa kuwa aka garzaya da shi [abokin nasa] har ɗakin, inda aka tarar da gawarsa zaune a kan kujera.

“Nan da nan aka sanar da ofishin ’yan sanda na Durumi kuma suka zo suka ɗauki hotuna da sauraren ababen da su taimaka musu wajen gudanar da bincike.”

Sanarwar ta ƙara da cewa, a halin yanzu an miƙa gawar Mista Parradang zuwa Asibitin Ƙasa da ke Abuja domin ɗauka matakan da suka dace “yayin da ma’aikatan otel ɗin ke ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai a binciken da suka gudanarwa.”

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Fashi Da Makami Sun Kashe Tsohon Babban Kwanturolan Hukumar NIS A Abuja 
  • ‘A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice’
  • A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Ficen Nijeriya — ’Yan sanda
  • Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD Ta Ce Sauye-Sauyen Da Ke Faruwa A Amurka Zai Shafi Al-Amura Da Dama A Majalisar
  • Kasashen Larabawa Sun Yi Tir Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji A Gaza
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Gargadi Malaman Da Ba Sa Zuwa Aiki
  • Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu
  • Hamas: Babu Wani Karin Tattaunawa Da HKI, A Aiwatar Da Yarjeniyar Kamar Yadda Take