Leadership News Hausa:
2025-03-06@03:40:54 GMT

Xi Jinping Ya Halarci Bitar Tawagar Lardin Jiangsu

Published: 5th, March 2025 GMT

Xi Jinping Ya Halarci Bitar Tawagar Lardin Jiangsu

Da yammacin yau Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarci bitar rahoton aikin gwamnatin kasar, na tawagar lardin Jiangsu, a taro na uku na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14.

Xi ya jaddada cewa, a matsayinsa na lardi mai karfin tattalin arziki, dole ne lardin Jiangsu ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta ci gaban kasar Sin, musamman ma a fannin sa kaimi ga inganta kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha, da dunkulewar masana’antu, da sa kaimi ga inganta zurfafa yin gyare-gyare, da bude kofa ga kasashen waje, da shigewa gaba wajen aiwatar da manyan tsare-tsare na ci gaban kasar, da kuma ba da misali a fannin samar da wadata ga jama’a baki daya.

(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An horas da masu unguwannin Katsina kan sasanta jama’a

Masarautar Katsina ta ba wa dagattai da masu unguwaninta horo a kan sasanta jama’a a matsayin ginshikin samun dauwamammen zaman lafiya.

An gudanar da taron ilmantarwar na tsawon kwanaki uku ne a kan yadda za a assasa zaman lafiya a tsakanin al’umma ta hanyar sasanci don samun aminci mai dorewa.

Shugaban kamfanin tuntuba na Green Horizon, Farfesa Muhammed Sabiu (SAN) ne ya jagoranci taron wanda shirin Kungiyar Kasashe Rainon Ingila ta shirya.

Tun da farko a jawabinsa na bude taron, Sarkin Katsina, Dokta Abdulmuminu Kabir Sarkin Fulani Hamceta Alhaji Aminu Lawal Bagiwa ya wakilta, ya ja hankalin mahalarta da su tsaya domin sanin abin da za a ilmantar da su kasancewarsu na shugabannin al’umma kuma na farko da ake kawo wa koke.

Ramadan: Gwamnatin Jigawa ta rage lokacin aiki Miji ya yi yunƙurin kashe matarsa kan zargin maita a Kano NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba

A nasa bangaren, Gwamnan Katsina, Umar Dikko Radda wanda Sakataren gwamnatin jahar Barista Abdullahi Garba Faskari ya wakilta ya ce, babu yadda za a samu ci gaban gal’umma sai in tana da zaman lafiya.

Ya ce, kara wa juna ilmi a kan abin da ya shafi zaman lafiya ba karamin abu ba ne, domin an samu wani ilmin da ba’a da shi, saboda haka, “ina kara jan hankalinku da ku tsaya domin amfana da abinda za a koya maku.”

Daya daga cikin mahalarta taron, Mai Unguwa Abubakar ya ce, tabbas “A yanzu na kara samun ilmin yadda zan warware wasu matsaloli idan sun taso a cikin jama’a ta ba sai anje ko’ina ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NOA Ta Kara Daura Damarar Inganta Ayyukanta A Jihar Jigawa
  • ’Yan sanda sun ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a Gombe
  • Har Kullum Jama’ar Kasar Sin Suna Adawa Da Nuna Fin Karfi
  • Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Batutuwan Da Suka Shafi Sinadarin Fentanyl
  • Dorawa Wasu Laifi Ba Zai Kawo Ci Gaban Da Amurka Ke Muradi Ba
  • Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya
  • An horas da masu unguwannin Katsina kan sasanta jama’a
  • Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran
  • Tawagar ECOWAS Ta Fice Daga Guinea-Bissau Bayan Barazana Daga Shugaban Kasar