Majalisar Kano ta yi wa dokar hukumar tace fina-finai gyaran fuska
Published: 5th, March 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta amince da yi wa dokar da ta kafa Hukumar Tace Fina-finai ta jihar gyare-gyare.
Ɗaya daga cikin sabbi gyaran da aka yi mata shi ne na wajabta wa masu wuraren bukukuwa da taruka yin rajista da hukumar.
Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan AkpabioWannan mataki ya zo ne saboda yadda ayyukan hukumar ke jan hankali, inda sau da yawa ake samun saɓani tsakaninta da wasu.
Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawal Husaini Dala ne, ya bayyana cewa an yi wannan dokar gyara ne don daidaita harkokin ɗaukar fina-finai da kare addini da al’adu.
Ya ce daga yanzu ba wanda zai iya ɗaukar fim a Kano ba tare da izinin hukumar ba.
A nasa ɓangaren, Shugaban Hukumar Tace Fina-finai ta Kano, Abba El-Mustapha, ya gargaɗi masu wallafa bidiyo a shafukan sada zumunta da su guji duk wani abu da zai taɓa mutuncin addini, al’adun Hausawa, ko kuma darajar al’ummar Kano.
Ya ce hukumar za ta mara wa masu ƙirƙirar bidiyo na nishaɗi da kasuwanci, amma ba ga waɗanda ke amfani da kafafen sada zumunta don cin mutunci ba.
Haka kuma, El-Mustapha ya bayyana cewa hukumar tana da ikon ɗaukar mataki kan duk wani abu da ya saɓa wa al’adu da addini, musamman idan aka samu ƙorafi.
Yanzu haka dai majalisar dokokin jihar ta kammala nata aikin, saura gwamnan Kano ya sanya hannu a kan dokar domin ta fara aiki.
Sai dai har yanzu ba a tantance lokacin da gwamnan zai rattaɓa hannu a kai ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki
Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki domin tallafa wa mabuƙata a wannan wata mai albarka na Ramadana.
Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya ƙaddamar da rabon abincin a cibiyar Dandali da ke Ƙaramar Hukumar Fagge a jihar.
HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarkiBayanai sun ce gwamnatin jam’iyyar NNPP ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf da ta ƙaddamar da wannan shiri tana da burin raba abincin buɗa-baki ga mabuƙata masu azumtar watan Ramadana.
Gwamnatin ta ce an tanadi cibiyoyi 91 domin raba wa mabuƙata 91,000 abincin buɗa-baki duk rana nan da tsawon kwanaki 27 masu zuwa.
Domin tabbatar da samun nasara, gwamnatin ta ce ta ɗauki masu aikin girke-girke da za su riƙa dafawa sannan su raba wa mabuƙata abincin.
Mataimakin Gwamnan wanda shi ne ke jagorantar shirin raba abincin a bana, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka ƙaddamar da shirin, yana mai kiran waɗanda aka ɗora wa alhakin aikin su tabbatar da raba wa mabuƙata abincin a kan kari.
Aminiya ta ruwaito cewa, Mataimakin Gwamnan ya samu rakiyar wasu ƙusoshin Gwamnatin Kano wajen ƙaddamar da rabon abincin da suka haɗa da Kwamishinan Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya da Kwamishinan Harkokin Addini, Sheikh Tijjani Auwal da sauransu.
Gwamnatin Kano ta jaddada ƙudirinta na rage raɗaɗin al’umma musamman Musulmi a wannan wata mai falala.