Aminiya:
2025-03-06@09:18:41 GMT

Mutum 2 sun rasu, 6 sun jikkata yayin da gini ya rufta a Legas

Published: 6th, March 2025 GMT

Wani gini mai hawa biyu ya rufta a yankin Lekki da ke Jihar Legas wanda ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu shida.

Jami’an bayar da agaji daga hukumomin LASEMA da NEMA sun ceto waɗanda suka jikkata kuma an kai su Babban Asibitin Marina domin kula da lafiyarsu.

Majalisar Kano ta yi wa dokar hukumar tace fina-finai gyaran fuska Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan Akpabio

Tun da farko, ’yan sanda sun ce an ceto mutum 14 daga wajen da ginin ya rufta.

Sakataren hukumar LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa ana bincike don gano musabbabin rushewar ginin.

“Zuwa yanzu mun gano gawarwakin mutum biyu daga cikin baraguzan gini, yayin da aka kai mutum shida da suka jikkata zuwa asibiti,” in ji shi.

“Ana ci gaba da gudanar da ayyukan ceto domin gano waɗanda lamarin ya rutsa da su.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ruftawar gini

এছাড়াও পড়ুন:

Hasashe Kan Tarukan CPPCC Da NPC Na 2025

Taron kwamitin ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar Sin (CPPCC) da za a fara ranar 4 ga watan Maris, da na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin (NPC) da za a fara ranar 5 ga watan Maris, su kasance manyan taruka biyu na kasar Sin inda ake gangamin siyasa domin nazartar baya da kuma hangen gaba. Wadannan hukumomi biyu suna karkashin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wadda ke karkashin jagorancin babban sakataren Xi Jinping. Kwamitin CPPCC na kasa, mai mambobi 2,169, yana aiki ne a matsayin babbar hukumar da ke tafiyar da tsarin dunkulewar sassan kasar ta fuskar siyasa, wanda ke hada kungiyoyin zamantakewa daban daban mashawarta jam’iyyar. Ita kuma, majalisar NPC mai wakilai 2,977, tana aiki ne a matsayin majalisa guda, kuma babbar majalisar dokokin kasar.

Hasashen manazarta kan taruka na bana na da alaka da wani taron karawa juna sani wato “taro kan kamfanoni masu zaman kansu” wanda shugaba Xi ya karbi bakunci a ranar 17 ga watan Fabrairu, wanda ya samu halartar manyan ’yan kasuwa na kasar. A shekarar 2018 ne aka fara gudanar da irin wannan taro da ya kasance na musamman wanda ke kara wa tattalin arzikin kasar karfin gwiwa, musamman bayan dawowar shugaba Trump na Amurka a karo na biyu, wanda ya ayyana kansa a matsayin “sarkin kakaba haraji”, wanda tuni ya sanya karin harajin kashi 10 cikin 100 kan kayayyakin Sin da ke shiga kasarsa. Yanzu, hankalin mahukunta ya karkata kan yadda Sin za ta kara kuzari, da tallafawa kasuwanci da kamfanoni, da kuma mayar da martani ga manufofin cinikayya na Trump.

Ana sa ran tarukan biyu za su bayyana ajandar da za ta kara habaka ci gaba idan aka kwatanta da bara, tare da hasashen kusan kashi 5% na ci gaban GDP, da kashi 4% na GDP na gibin kasafin kudi, da kashi 2% na hauhawar farashin kayayyaki. Bugu da kari, ana sa ran za a samu karin lamuni na kusan yuan tiriliyan 3 daga asusun baitulmali na musamman da kuma yuan tiriliyan 4.5—-5 daga lamuni na musamman na kananan hukumomi. Ta hakan za a gabatar da matakan da za su bunkasa sayayya da karfafa kamfanoni cikin gida masu zaman kansu a fannin kirkire-kirkire. Kazalika, ana sa ran za a tabo batutuwan da suka shafi ci gaban kamfanonin waje masu zaman kansu, da manufofin kasashen wajen musamman wadanda suka shafi batun Taiwan da yadda za a mayar da martani ga hauragiyar Trump. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 2 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Gini Ya Rufta A Legas
  • Kasar Sin A Matsayin Katafariyar Cibiyar Kere-Keren Mutum-Mutumi A Duniya
  • ’Yan sanda sun ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a Gombe
  • Ba Za Mu Tattauna da Rasha Ba Sai Ta Daina Kai Mana Hari – Zelensky
  • Manazarta A Iran Sun Gano Maganin Farfadiya Da Ciwon Rabin Kai
  • Hasashe Kan Tarukan CPPCC Da NPC Na 2025
  • An sake zaɓen Obasa Kakakin Majalisar Legas
  • An sake naɗa Obasa Kakakin Majalisar Legas
  • Ya rasu a yayin buɗa-baki a Abuja