Aminiya:
2025-04-07@20:44:25 GMT

Mutum 2 sun rasu, 6 sun jikkata yayin da gini ya rufta a Legas

Published: 6th, March 2025 GMT

Wani gini mai hawa biyu ya rufta a yankin Lekki da ke Jihar Legas wanda ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu shida.

Jami’an bayar da agaji daga hukumomin LASEMA da NEMA sun ceto waɗanda suka jikkata kuma an kai su Babban Asibitin Marina domin kula da lafiyarsu.

Majalisar Kano ta yi wa dokar hukumar tace fina-finai gyaran fuska Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan Akpabio

Tun da farko, ’yan sanda sun ce an ceto mutum 14 daga wajen da ginin ya rufta.

Sakataren hukumar LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa ana bincike don gano musabbabin rushewar ginin.

“Zuwa yanzu mun gano gawarwakin mutum biyu daga cikin baraguzan gini, yayin da aka kai mutum shida da suka jikkata zuwa asibiti,” in ji shi.

“Ana ci gaba da gudanar da ayyukan ceto domin gano waɗanda lamarin ya rutsa da su.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ruftawar gini

এছাড়াও পড়ুন:

Sau Biyu Ake Yin Girbin Aya A Shekara – RMRDC

A bisa wannan dalili ne yasa akwai bukatar mutane su rungumi fannin noman Aya, duba da cewa; hanya ce ga wanda ya zuba jarinsa a fannin, zai iya kara samar wa da kansa kudaden shiga.

Sai dai, akasari an fi yin nomanta a Arewacin Nijeriya, musamman ma kuma a Jihar Katsina.

Haka zalika, fannin na samar da ayyukan yi kodai na kai tsaye ko kuma wanda ba na kai tsaye ba.

Bugu da kari, Aya na taimawa wajen inganta lafiyar jikin Dan’adam, kara karfafa kashin jikin mutum, daidaita sigan da ke jikin bil Adama da dai sauran makamantansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
  • Ambaliya Ta Hallaka Mutum 30 A Birnin Kinshasa Na Jamhuriyar Demokradiyar Congo
  • HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas
  • Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC
  • Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno
  • Sau Biyu Ake Yin Girbin Aya A Shekara – RMRDC
  • Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
  • An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe
  • An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe