Gwamna Namadi Ya Karbi Lasisin Yin Kasuwanci Maras Shinge A Kan Iyakar Maigatari
Published: 6th, March 2025 GMT
Gwamna Mallam Umar Namadi na jihar Jigawa ya karbi lasisin yin hada hadar kasuwanci na kasa da kasa, wato kasuwanci maras shinge a kan iyakar Maigatari a hukumance, wanda hukumar kula da sarrafa kayayyaki ta Najeriya NEPZA ta bayar kwanan nan.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Hamisu Mohammed Gumel ya rabawa manema labarai a Dutse.
Ya bayyana cewa, kwamishinan kasuwanci, da masana’antu, Alhaji Aminu Kanta ne ya mika wa Gwamna Umar Namadi lasisin a ofishinsa.
Hamisu Mohammed Gumel ya bayyana cewa, tun lokacin da aka kafa wannan gwamnati mai ci ta dukufa wajen gudanar da aikin karbar lasisin aikin daga NEPZA
A cewarsa, wannan ya nuna karara da kudurin gwamnati na bunkasa tattalin arziki, da inganta harkokin kasuwanci, da kuma sanya jihar Jigawa a matsayin babbar cibiyar zuba jari da bunkasa masana’antu.
Sakataren yada labaran ya yi nuni da cewa, kafa harkar cinikayya a kan iyakar Maigatari na da nufin jawo hankalin masu zuba jari na gida da waje, da inganta samar da ayyukan yi, da bunkasa harkokin kasuwanci, musamman a yankin arewacin Najeriya.
Ya ce, Gwamna Namadi ya nuna jin dadinsa ga kokarin hadin gwiwa da ya kai ga samun lasisin tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na samar da yanayi mai kyau don gudanar da kasuwanci yadda ya kamata.
Hamisu ya yi nuni da cewa, a karkashin gwamnatin Gwamna Umar Namadi, wannan yunkuri ya samu gagarumin ci gaba da nufin bunkasa tattalin arziki da habaka masana’antu a jihar.
Kwamishinan ya samu rakiyar Kodineta na shiyyar kasuwanci maras shinge ta Maigatari, Abdulaziz Usman Abubakar da mai kula da shiyyar Bello Abdullahi Nura.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce a yanzu jihar na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya.
Ya ce, a matsayinsa na babban jami’in shari’a da tsaro a Jihar Yobe, yana da haƙƙin ganin an bi doka don tabbatar da cewa jihar ta samu zaman lafiya.
An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a YobeGwamnan ya bayyana hakan ne a yayin karɓar lambar karramawa da aka yi masa shi da wasu shugabnnin da Ƙungiyar Inganta zaman lafiya ta “Peace Building Development Consult” (PBDC) ta yi musu.
Gwamnan wanda ya samu wakilcin babban lauya kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Yobe, Barista Saleh Samanja, ya bayyana hakan ne ga manema labarai ranar Laraba a Abuja, bayan da ya karɓi lambar yabon ta zaman lafiya.
“ina tabbatar muku kai tsaye cewar, Jihar Yobe tana ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya, hakan yana yiwuwa ne saboda haɗin kan da muke bai wa jami’an tsaro da kuma namijin ƙoƙarin da Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ke yi na bada gudummawa kan harkokin tsaro da duk abin da hukumomin tsaro ke son gwamnati ta yi.
“A matsayinsa na babban jami’in shari’a da tsaro na jihar, yana jin cewa yana da haƙƙin ɗabi’a da na shari’a don ba da haɗin kai ga hukumomin tsaro domin mu samu cikakken zaman lafiya a Jihar Yobe,” in ji shi.
A cewarsa wannan karramawar na ƙara ƙarfafa gwiwa ne, inda ya ce Gwamnan zai ci gaba da yin abin da yake yi domin ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.