Aminiya:
2025-03-06@12:42:50 GMT

NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba?

Published: 6th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Fiye da wata guda ke nan bayan da Matatar mai ta Ɗangote ta sanar da rage farashin man fetur daga naira 890 zuwa naira 825 kowace lita.

Bayan wannan ragi ne dai shi ma Kamafanin Mai na Kasa (NNPCL) ya sanar da rage nasa farashin. Sai dai  har yanzu ba a ga ragin a gidajen mai  ba.

NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan wannan lamari.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Ramadan: Gwamnatin Jigawa ta rage lokacin aiki

Gwamnatin Jihar Jigawa ta rage tsawon lokacin aikin ma’aikatanta nan take albarkacin watan Ramadan.

Gwamna Umar Namadi ya dauki matakin ne domin ba wa ma’aikata damar samun hutut da kuma  gudanar da ibada a wannan wata mai albarka.

Shugaban Ma’aikata na jihar, Muhammad Kandira Dagaceri, ya sanar da cewa ce daga yanzu lokacin aiki ya koma karfe 9 na safe zuwa 3 na yamma a ranakun Litinin zuwa Alhamis.

Sanarawar ta kara da cewa ranar Juma’a kuma za a rika tashi aiki karfe 1 na rana har zuwa karshen watan azumin.

Ya kuma yi kira ga ma’aikata da su yi amfani da watan ibadar wajen yin addu’o’in samun sauki a fannin tattalin arziki da zaman lafiya a Jihar Jigawa da ma kasa ba ki daya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Azumin Ramadan: Hauhawar farashin ‘ya’yan itace na damun masu lura da Ramadan
  • Ramadan: Gwamnatin Sakkwato Ta Rage Wa Ma’aikata Lokacin Aiki
  • Azumin Ramadan: Gwamna Buni Ya Amince Da Naira Miliyan 297 Don Ciyar Da Mutane 51,000 A Kullum
  • EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Akwa Ibom kan almundahanar Naira biliyan 700
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar
  • Majalisar Zartarwa Ta Tarayyar Najeriya Ta Amince Da Kirkirar Sabbin Jami’oi 11
  • Ramadan: Gwamnatin Jigawa ta rage lokacin aiki
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba
  • An Fara Haska Fim Din Sin A Sinimomin Najeriya Da Ghana Da Laberiya