NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba?
Published: 6th, March 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Fiye da wata guda ke nan bayan da Matatar mai ta Ɗangote ta sanar da rage farashin man fetur daga naira 890 zuwa naira 825 kowace lita.
Bayan wannan ragi ne dai shi ma Kamafanin Mai na Kasa (NNPCL) ya sanar da rage nasa farashin. Sai dai har yanzu ba a ga ragin a gidajen mai ba.
Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan wannan lamari.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Ramadan: Gwamnatin Jigawa ta rage lokacin aiki
Gwamnatin Jihar Jigawa ta rage tsawon lokacin aikin ma’aikatanta nan take albarkacin watan Ramadan.
Gwamna Umar Namadi ya dauki matakin ne domin ba wa ma’aikata damar samun hutut da kuma gudanar da ibada a wannan wata mai albarka.
Shugaban Ma’aikata na jihar, Muhammad Kandira Dagaceri, ya sanar da cewa ce daga yanzu lokacin aiki ya koma karfe 9 na safe zuwa 3 na yamma a ranakun Litinin zuwa Alhamis.
Sanarawar ta kara da cewa ranar Juma’a kuma za a rika tashi aiki karfe 1 na rana har zuwa karshen watan azumin.
Ya kuma yi kira ga ma’aikata da su yi amfani da watan ibadar wajen yin addu’o’in samun sauki a fannin tattalin arziki da zaman lafiya a Jihar Jigawa da ma kasa ba ki daya.