Mutanen Afrika Sun Kori Kasar Faransa Daga Kashensu Ne Saboda Ta Ki Ta Amince Da Yencinsu
Published: 6th, March 2025 GMT
Pierre de Gaulle, dan tsohon shugaban kasar Faransa Charles de Gaulle, wanda ya jagoranci kasar Faransa a samun yencin kasar daga hannun sojojin NAZi a yakin duniya na biyu, ya bayyana cewa kasashen Afrika sun kore kasar Faransa daga kasashensu ne bayan da kasar ta kasa yin abinda zai kawo ci gaban kasashen.
Kamfanin dillancin labaran Spunik na kasar Rasha ya nakalto jikan de Gaulle yace tsarin kasar Faransa na tattalin arziki da siyasa sun sanya kasashen cikin talauci da rashin ci gaba. Wannan ya sa suka zabi korar kasar Faransa daga kasashensu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Faransa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Gudun Hijiran Sudan Sun Yi Kira Ga Kungiyoyin Kasa Da Kasa Da Su Ceto Yara Da Tsofaffi Daga Mummunan Kangi A Sudan
‘Yan gudun hijira a Sudan sun yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su ceto yara da tsofaffi daga mummunan kangin da suka shiga
An gwabza kazamin fada a kusa da birnin El Fasher da ke arewacin Darfur tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, wadanda suka yi ruwan bama-bamai kan birnin da na manyan bindigogi, inda suka kashe fararen hula akalla 35.
Sojojin Sudan sun samu nasarar dakile wadansu daga cikin wadannan hare-hare, amma duk da haka sun janyo hasarar rayukan bil’adama da na dukiya. Sannan sojojin Sundan sun kuma kwace iko da birnin Bara da ke Arewacin Kordofan, kofar Nyala a Kudancin Darfur.
Dakarun kai daukin gaggawa sun yi wa birnin kawanya da nakiyoyi da ramuka da nufin yiwuwar harin farmakin sojojin Sudan.