Pierre de Gaulle, dan tsohon shugaban kasar Faransa Charles de Gaulle, wanda ya jagoranci kasar Faransa a samun yencin kasar daga hannun sojojin NAZi a yakin duniya na biyu, ya bayyana cewa kasashen Afrika sun kore kasar Faransa daga kasashensu ne bayan da kasar ta kasa yin abinda zai kawo ci gaban kasashen.

Kamfanin dillancin labaran Spunik na kasar Rasha ya nakalto jikan de Gaulle yace tsarin kasar Faransa na tattalin arziki da siyasa sun sanya kasashen cikin talauci da rashin ci gaba. Wannan ya sa suka zabi korar kasar Faransa daga kasashensu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Faransa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ta Amince Da Gazawarta Wajen Hana Harin Hamas

Hukumar leken asiri ta gwamnatin Isra’ila (Shin Bet) ta amince da gazawarta wajen hana harin ba-zata da kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, 2023.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Talata, shugaban hukumar ta Shin Bet, Ronen Bar, ya amince da cewa, hukumar ta ” gaza a cikin aikinta” na dakile ayyukan Operation Al-Aqsa, tare da kutsawa manyan sansanonin Isra’ila bayan da sojoji da ‘yan sandan gwamnatin suka yi kaca-kaca da su.

Ya ce, da hukumar ta Shin Bet ta yi wani abu daban a cikin shekarun da suka gabata kafin harin da kuma a daren da aka kai harin… da an kaucewa hakan.

“A matsayina na shugaban hukumar, zan dauki wannan nauyi a wuyana har karshen rayuwata,” in ji shi.

Hukumar ta amince da gagarumin gibi a cikin tattara bayanan sirri da kuma dogaro da matakan kariya da ake da su, wanda ya haifar da rashin fahimtar kungiyar Hamas, tare da sauran kungiyoyin gwagwarmaya.

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wani “binciken cikin gida” ya nuna cewa, an gaza wajen dakile harin na Hamas.

Binciken da sojojin Isra’ila suka gudanar ya soki yadda gwamnatin kasar ke dogaro da bayanan sirri da kuma raina karfin Hamas, kura-kuran da suka haifar da mummunan sakamako ga gwamnatin Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jakadan Iran A Hukumar IAEA Ya Ce Takunkuman Kasashen Yamma A Kan Kasar Ba Za Su Yi Aiki Ba
  • Wata Kotu A Iran Ta Ci Taran  Gwamnatin Amurka Dala Biliyon $12.6 Saboda Haddasa Mutuwar Masu Fama Da Cutar ‘thalassemia’ A Kasar
  • Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ta Amince Da Gazawarta Wajen Hana Harin Hamas
  • Taron Kasashen Turai Don Goyon Baya Ga Kasar Ukraine, Ya Watse Ba Tare Da Tsaida Irin Taimakon Da Zasu Yi Mata Ba
  • Kremlin: Putin Ya Amince Da Shiga Tsakanin Iran Da Amurka
  • Majalisar Zartarwa Ta Tarayyar Najeriya Ta Amince Da Kirkirar Sabbin Jami’oi 11
  • DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana
  • Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran
  • Tawagar ECOWAS Ta Fice Daga Guinea-Bissau Bayan Barazana Daga Shugaban Kasar