Majiyar Fadar Shugaban Kasar Amurka Tace Ta Shiga Tattaunawa Kai Tsaye Da Kungiyar Hamas A Gaza
Published: 6th, March 2025 GMT
Sakataren watsa labarai na Fadar white House ta tabbatar da cewa gwamnatin Amurka ta shiga tattaunawa da kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza kai tsaye.
Tashar talabijin ta Presstv a nann Tehran ta nakalto Karoline Leavitt tana fadar haka a jiya Laraba, ta kuma kara da cewa, shugaban kasar Amurka Donal Trump ya aiki Adam Boehler mutumin da yake wakiltansa a al-amuran fursinonin Amurka a waje, zuwa kasashen yankin kudancin Asiya don tattauna batun Amurkawa da suke hannun kungiyar Hamas a Zirin Gaza.
Leavitt ta kara da cewa Amurkawa sun cancanci a shiga tattaunawa ko kuma a bi duk hanyoyin da suka dace don ganin, an kubutar da Amurka wadanda suka shiga hanun makiyansu a ko ina suke a duniya.
Wannan labarin yana zuwa ne a lokacinda fadar ta white hause ta bayyana kungiyar Hamas a matsayin kungiyar yan ta’adda.
Hamas ta fara kama Amurkawa ta tsare tun shekara 1997 bayan da Amurka ta fito fili tana goyon bayan HKI kan kisan kiyashin da takewa Falasdinawa a Gaza da sauran wurare.
Rahoton ya kara da cewa Amurka ta fara tattaunawa da kungiyar ne a birnin Doha na kasar Qatar a cikin yan makonnin da suka gabata.
A halin yanzu dai Hamas tana rike da fursinoni 59 daga cikin 240 da suka kama a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kungiyar Hamas
এছাড়াও পড়ুন:
Matsin Tattalin Arziki Ya Karfafa Mana Gwiwar Raba Tallafi Ramadan – Sarkin Fada
Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ, FRCN Kaduna Chapel, ta jaddada kudirinta na inganta jin dadin mambobinta ta hanyar bullo da sabbin tsare-tsare da shirye-shiryen tallafi.
Shugaban kungiyar, Kwamared Umar Adamu Sarikin Fada ne ya bayyana haka a lokacin rabon kayan abinci na Ramadan ga ‘yan kungiyar a Kaduna.
Umar Adamu Sarikin Fada ya bayyana cewa shirin rabon kayayyakin na daga cikin dabarun da kungiyar ta keyi na dakile tasirin tabarbarewar tattalin arzikin kasar nan.
Ya tabbatar da cewa sama da ‘yan uwa Musulmi dari da hamsin ne suka ci gajiyar shirin na watan Ramadan na bana, inda ya jaddada cewa su ma Kirista na kungiyar sun samu irin wannan tallafi a lokacin bukukuwan Kirsimeti na 2024.
Shugaban ya kuma yi kira ga mambobin kungiyar da su sake sadaukar da kansu wajen gudanar da ayyukansu domin ci gaban FRCN da kasa baki daya.
REL/MANSUR S PAKI