Majiyar Fadar Shugaban Kasar Amurka Tace Ta Shiga Tattaunawa Kai Tsaye Da Kungiyar Hamas A Gaza
Published: 6th, March 2025 GMT
Sakataren watsa labarai na Fadar white House ta tabbatar da cewa gwamnatin Amurka ta shiga tattaunawa da kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza kai tsaye.
Tashar talabijin ta Presstv a nann Tehran ta nakalto Karoline Leavitt tana fadar haka a jiya Laraba, ta kuma kara da cewa, shugaban kasar Amurka Donal Trump ya aiki Adam Boehler mutumin da yake wakiltansa a al-amuran fursinonin Amurka a waje, zuwa kasashen yankin kudancin Asiya don tattauna batun Amurkawa da suke hannun kungiyar Hamas a Zirin Gaza.
Leavitt ta kara da cewa Amurkawa sun cancanci a shiga tattaunawa ko kuma a bi duk hanyoyin da suka dace don ganin, an kubutar da Amurka wadanda suka shiga hanun makiyansu a ko ina suke a duniya.
Wannan labarin yana zuwa ne a lokacinda fadar ta white hause ta bayyana kungiyar Hamas a matsayin kungiyar yan ta’adda.
Hamas ta fara kama Amurkawa ta tsare tun shekara 1997 bayan da Amurka ta fito fili tana goyon bayan HKI kan kisan kiyashin da takewa Falasdinawa a Gaza da sauran wurare.
Rahoton ya kara da cewa Amurka ta fara tattaunawa da kungiyar ne a birnin Doha na kasar Qatar a cikin yan makonnin da suka gabata.
A halin yanzu dai Hamas tana rike da fursinoni 59 daga cikin 240 da suka kama a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kungiyar Hamas
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan harkokin wajen Iran zai Ziyarci Saudiyya da Qatar
A wani lokaci a gobe Asabar ne ake sa ran ministan harkokin wajen Iran zai fara wata ziyara a kasashen Saudiyya da kuma Qatar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi zai ziyarci Saudiyya da Qatar a, bayan rahotannin da ke cewa akwai yiwuwar yin wata sabuwar tattaunawa tsakanin Tehran da Washington.
M. Baghai ya bayyana cewa ziyarce ziyarce da Araghchi zai yi na daga cikin manufofin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na ci gaba da karfafa alakarta da makwabtanta.
“Ministan harkokin wajen kasar ta Iran, zai fara tafiya birnin Riyadh don ganawa da manyan jami’an Saudiyya, sannan kuma zai tafi Doha don halartar taron tattaunawa tsakanin Iran da kasashen Larabawa.”
Bayanin hakan ya biyo bayan rahoton da kafar yada labaran Amurka Axios ta bayar cewa, ranar Lahadi ne ake sa ran za a gudanar da zagaye na hudu na tattaunawar tsakanin Iran da Amurka a birnin Muscat na kasar Omani.
Tun da farko dai an shirya gudanar da taron ne a ranar 3 ga watan Mayu, amma aka dage.