Jakadan JMI a hukumar makamashin Nukliya Mohsen Naziri ya bayyana cewa sabbin takurawar da kasashen yamma, musamman Amurka suke wa kasarsa ba zasu yi tasiri ba. Banda hakan zasu cutar da wadanda suka dora mana su,

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Naziri yana fadar haka a Jawabin da ya gabatar  a taron gwamnoni hukumar ta IAEA a birnin Geneva a jiya Laraba.

Ya ce kasashen yamma ne suka jagoranci karin takunkuman tattalin arziki a kan Iran, ko kuma bayyana cewa Iran bata bada hadin kai da ta dace ga hukumar makamashin Nukliya ta duniya wato IAEA. Da kuma zargin kasar Iran da cewa tana kokarin mallakan makaman Nukliya.

Naziri ya zargin kasashne yamma kan rashin cika al-kawalin da suka dauka a yarjeniyar JCPOA na shekara ta 2015, inda Amurka ta fara da janyewa daga yerjeniyar da aka dauki shekaru biyu cur ana tattaunawa a kanta.

Yace Amurka ta fice daga yaerjeniyar a shekara ta 2018 da sunan shi ne yarjeniya mafi muni wanda Amurka ta taba sanyawa hannu, kuma zata tilastwa Iran amincewa da sabuwar yarjeniya da ita, ko kuma ta sha wahala, ko gwamnatin JMI ta rushe karkashin takurawar ta.

Banda haka kasashen Turai wadanda suke goyon bayan Amurka sun ki cika nasu alkawulan a cikin yarjeniyar ta JCPOA.

Naziri Asl ya bayyana cewa martanin da Iran ta mayar shi ne, rage abinda yah au kanta a yarjeniyar, , wanda ita kanta Yarjeniyar ta bada damar yin haka a duk lokacinda dayan bangaren ya saba alkawulan da ta dauka a cikinta.

Ka’ida ta 26 da 36 na yarjeniyar ta bawa Iran wannan damar, na sabawa yarjeniyar don dawo da dayan bangaren kan abinda yakamata ya yi.

Ya kuma kara da cewa kasashen yamma basu da damar sake maida takunkuman tattalin arziki kan Iran saboda sune suka sabawa yarjeniyar.

Daga karshe ya ce Iran zata koma kan amfani da yarjeniyar ne kawai idan kasashen yamma sun dauke mata dukkan takunkuma tattalin arzikin da suka dora mata.

Sannan yace kasashen Ingila Faransa da Jamus sun sabawa kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2231 wanda yake goyon bayan JCPOA.

Daga karshe yayi kira da gwamnonin hukumar ta IAEA da su maida hankalinsu wajen dabbaka kudurin na 2231.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen yamma a yarjeniyar

এছাড়াও পড়ুন:

Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja

Ana fargabar cewa wasu masu ta’adar garkuwa da mutane sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), David Shikfu Parradang a Abuja.

Majiyoyi sun shaida wa ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya Zagazola Makama cewa ’yan ta’addan sun ɗauke Parradang a yankin Area 1 da ke babban birnin ƙasar da safiyar wannan Talatar.

Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya Muhimmancin ƙamshi a rayuwar mace

Makama ya ce ’yan ta’addan sun biyo sawun tsohon babban jami’in Hukumar Shige da Ficen ne bayan ya ciro kuɗi a banki, inda suka karɓe kuɗin sannan kuma suka kashe shi.

Wannan lamari dai ya sake ɗaga hankalin mazauna Abuja a fannin tsaro musamman yadda a bayan nan ta’adar kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ƙara ƙamari.

Parradang dai ya shafe fiye da shekaru 30 yana aiki a Hukumar Shige da Ficen Nijeriya, inda ya riƙe muƙamai daban-daban a faɗin ƙasar cikin har da kujerar Kwanturola-Janar na ƙasa.

Ya yi aiki a jihohin Kano, Legas, Kwara, Enugu da Abuja, sannan ya yi kwasa-kwasai na neman ƙwarewa da sanin makamar aiki a nan cikin gida da ƙetare.

Tuni hukumomin tsaro suka soma gudanar da bincike domin bankaɗo masu hannu a wannan aika-aikar.

Kawo yanzu babu wata sanarwa da hedikwatar Hukumar Shige da Ficen ta fitar dangane da faruwar lamarin.

Sai dai wani jami’anta a hedikwatar da ke Abuja ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa a jira hukumar ta fitar da sanarwa a hukumance.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Yi Maraba Da Shirin Sake Gina Gaza Da Taron Kasashen Larabawa Ya Gabatar
  • Iran Ta Ce Dole Ne Amurka Ta Janye Mata Takunkuman Tattalin Arziki Masu Gurgurtawa Da Ta Dora Mata
  • Taron Kasashen Turai Don Goyon Baya Ga Kasar Ukraine, Ya Watse Ba Tare Da Tsaida Irin Taimakon Da Zasu Yi Mata Ba
  • Kremlin: Putin Ya Amince Da Shiga Tsakanin Iran Da Amurka
  • Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja
  • Masu Alaka
  • Hamas Ta Ce Yarjeniyar Tsagaita Wuta Ne Kadai Za Ta Kubutar Da Fursinonin Yahudawa Daga Hannun Kungiyar
  • Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Gargadi Malaman Da Ba Sa Zuwa Aiki