Aminiya:
2025-03-06@13:16:04 GMT

An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai

Published: 6th, March 2025 GMT

’Yan sanda sun kama wani korarren jami’in shige da fice a yayin da yake kokarin sayar da makamai Ga ’yan ta’adda.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Babban Birnin Tarayya, Olatunji Rilwan Disu, ya bayyana cewa an kama jami’in ne a hanyarsa ta kai wa ’yan ta’addan bindigogi a yankin Zuma da ke Ƙaramar Hukumar Bwari.

Da yake jawabi a hedikwatar rundunar, CP Olatunji Rilwan, ya bayyana cewa dubun korarren jami’in tsaron ta cika ne a ranar 27 ga watan Fabrairu, 2025.

Ya bayyana cewa jami’an rundunar yaki da masu garkuwa da mutane ƙarƙashin jagorancin OC Mustapha Muhammad ne suka kama shi, bayan samun bayanan sirri.

NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba? Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa

Disu wanda ke bayani kan ayyukan rundunar daga watan Janairu zuwa Maris na 2025, ya ce an ƙwato wasu sabbin manyan bindigogi biyu ƙirar CZ Scorpion EVO 3 A1 a hannun wanda ake zargin.

Ya bayyana cewa rundunar tana tsare da wanda ake zargin yana amsa tambayoyi

 

Ya kara da cewa rundunar yaƙi da masu garkuwa da mutanen ta kuma halaka wasu ’yan bindiga bakwai a wani samamen da ta kai maɓoyar ɓata-garin a ƙauyen Gidan-Dogo da Daji Kweri da ke kan iyakar Abuja da Jihar Neja.

Ya ce an kama ’yan bindiga ɗauke da bindigogi ƙirar AK47da sauran wasu makamai a yankunan.

AA cewarsa, jimillar ’yan fashi da makami 59 da masu garkuwa da mutane tara da masu kai musu bayanai 10 ne dubu su ta cika a tsawon lokacin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Tsaro Ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Alaka

Iran Tayi Tir Da Shirin Shugaban Amurka Na Sake Tsugunar Da Al’ummar Gaza

Kakakin gwamnatin kasar iran Fatime mohajerani ta yi tir da aniyar  shugaban Amurka Donald trumph na kwashe alummar gaza zuwa wasu  wurare, kuma ta biyyana shi a matsayin ci gaba da siyasar kisan kare dangi kan alumma falasdinu,

Shugaban na Amurka Donald trump yayi wannan bayanin ne a taron manema  labarai  da yayi a fadar white hause da fira ministan isra’ila binjamin natanyaho a watan jiya, inda ya nuna aniyarsa ta kwashe alumma yankin gasa zuwa wasu kasashen larabawa. Tare da gina wajen shakatawa da babbar tashar jiragen ruwa a wajen.

Shuwagabannin  kasashen laraba wa da na musulmi sun jadda mastayinsu na amincewa da yancin falasdinawa tare da yin watsi da duk wani yunkuri na rabasu da gidajensu.

Wasu masharhanta na ganin shirin na Amurka zai jawo a mata mayar da ita saniyar ware a harkokin diplomasiya har ma tsakaninta da sauran kawayenta a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Binuwai
  • A Kasar Sudan Ta Kudu  Jami’an Tsaro Sun Killace Gidan Mataimakin Shugaban Kasa
  • Hukumar Sibil Difens za ta ɗauki sabbin jami’ai
  • Sibil Difens za ta da ɗauki sabbin ma’aikata
  • An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna
  • Ana zargin wata mata da kashe kishiyarta a Bauchi
  • Wata mata ta kashe kishiyarta a Bauchi
  • Masu Alaka
  • Jami’an tsaro sun hana jama’a kwasar mai bayan hatsarin tanka a Taraba