Leadership News Hausa:
2025-03-06@12:43:30 GMT

Mutum 2 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Gini Ya Rufta A Legas

Published: 6th, March 2025 GMT

Mutum 2 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Gini Ya Rufta A Legas

Hukumar LASEMA ta bayyana cewa tawagarta ta fara aikin ceto da bincike tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin agaji.

Haka kuma, an tura manyan motocin tono ƙasa don taimakawa wajen share baraguzan ginin da kuma ceto duk wanda ya maƙale a ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ruftawa

এছাড়াও পড়ুন:

Fasinjoji 16 sun ƙone ƙurmus a Ogun

Aƙalla fasinjoji 16 suka ƙone ƙurmus, yayin da wasu uku suka jikkata a wani hatsarin mota da ya afku ranar Talata a Jihar Ogun.

Aminiya ta ruwaito cewa hadarin wanda ya rutsa da mota ɗaya kacal ya afku ne a gidan Buhari da ke kan titin Abeokuta zuwa Shagamu.

DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana ‘A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice’

An bayyana cewa, hatsarin dai ya rutsa da wata farar motar bas kirar Mazda mai lamba KJA 949 YJ, da misalin ƙarfe 1:00 na rana.

Kakakin Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), Florence Okpe, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar.

Ta ce ba za a iya tantance jinsin waɗanda abin ya shafa ba saboda “sun ƙone ƙurmus ta yadda ba a iya fahimtar halittar jikinsu ba.”

Okpe ta ɗora alhakin faruwar hatsarin a kan gobarar da ta tashi a cikin motar, tana mai cewa bas ɗin tana ɗauke da fasinjoji 21 da kuma wata tukunyar gas wadda ta yi bindiga a cikin motar.

“Hatsarin ya rutsa ne da mutane 21. Ba a iya tantance waɗanda abin ya shafa ba saboda sun ƙone ba a iya gane su ba.

“Mutane 16 ne suka mutu a hatsarin, yayin da uku suka samu raunuka daban-daban, sai kuma wasu biyu suka tsallake rijiya da baya.

“Abinda ake zargin ya haddasa hadarin shi ne gobarar da ta tashi a cikin motar, wadda kuma tana ɗauke da wata tukunyar gas, wanda ya kai ga fashewar,” in ji ta.

Okpe ta ce an kai waɗanda suka jikkata zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Idi Aba a birnin Abeokuta.

Kwamandan Hukumar FRSC na yankin, Akinwumi Fasakin, yayin da yake jajantawa iyalan mamatan, ya yi gargaɗin cewa, ya kamata a riƙa safarar kayan da ka iya jawo tashin wuta cikin kulawa da kuma motocin da aka keɓe waɗanda ƙwararru direbobi ke tuƙawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe Ƙwararren Mai Haɗa Wa Boko Haram Bam A Borno
  • Mutum 2 sun rasu, 6 sun jikkata yayin da gini ya rufta a Legas
  • Kasar Sin A Matsayin Katafariyar Cibiyar Kere-Keren Mutum-Mutumi A Duniya
  • An Koya Min Girmama Mata – Akpabio Ya Musanta Zargin Cin Zarafin Natasha
  • ’Yan sanda sun ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a Gombe
  • Fasinjoji 16 sun ƙone ƙurmus a Ogun
  • Sin Za Ta Kakaba Karin Harajin Kwastam Kan Wasu Kayayyakin Amurka
  • Ba Za Mu Tattauna da Rasha Ba Sai Ta Daina Kai Mana Hari – Zelensky
  • Meranda Ta Yi Murabus, Obasa Ya Sake Zama Kakakin Majalisar Dokokin Legas