Leadership News Hausa:
2025-04-07@20:26:57 GMT

Mutum 2 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Gini Ya Rufta A Legas

Published: 6th, March 2025 GMT

Mutum 2 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Gini Ya Rufta A Legas

Hukumar LASEMA ta bayyana cewa tawagarta ta fara aikin ceto da bincike tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin agaji.

Haka kuma, an tura manyan motocin tono ƙasa don taimakawa wajen share baraguzan ginin da kuma ceto duk wanda ya maƙale a ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ruftawa

এছাড়াও পড়ুন:

An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe

Wasu ’yan bindiga sun kai hari kan wata motar bas ta sufurin fasinja ta Benue Links da ke kan hanyarta a titin Ikobi na ƙaramar hukumar Otukpo a Jihar Benuwe, inda suka kashe direban da wani fasinja na gaba, yayin da suka yi awon gaba da wasu fasinjojin.

Lamarin ya afku ne da yammacin ranar Alhamis a kusa da rusasshen kamfanin Benue Burnt Bricks, wanda aka fi sani da hanyar shiga garin Otukpo.

’Yan sanda sun gayyaci Sarki Sanusi domin amsa tambayoyi Motar fasinja ta kama wuta wasu sun tsallake rijiya da baya

Motar mallakar gwamnatin Jihar ta kamfanin Benue Links Nigeria Limited tana kan hanyar Makurdi zuwa Otukpo lokacin da aka yi mata kwanton ɓauna.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na kamfanin, Johnson Ehi Daniel ya fitar a ranar Juma’a, ya tabbatar da faruwar harin, ya kuma yaba da yadda jami’an tsaro suka mayar da martani cikin gaggawa, tare da bayyana ƙwarin gwiwar ci gaba da ƙoƙarin kuɓutar da fasinjojin da aka sace.

“Benue Links Nigeria Limited ta yi takaicin sanar da harin da aka kai kan wata motar safa mai lamba PP512. Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Alhamis, 3 ga watan Afrilu, 2025, kusa da Otukpo Burnt Bricks lokacin da wasu mahara ɗauke da makamai suka yi wa motar kwanton ɓauna.

“Abin takaici, maharan sun harbe direban motar bas mai kujeru 18, Mista Samuel Agege da wani fasinja na gaba, yayin da ’yan bindigar suka yi yunƙurin sace sauran fasinjojin, wasu mutane uku sun yi nasarar tserewa, wani kuma ya sauka tun da farko a garin Taraku kafin faruwar lamarin,” in ji sanarwar.

Hukumomin kamfanin sufurin sun jajantawa iyalan waɗanda suka rasu tare da yin alƙawarin ci gaba da haɗa kai da jami’an tsaro domin ganin an dawo da fasinjojin da aka sace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka 
  • An Samu Karuwar Tafiye Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Qingming Na Sin
  • An Samu Karuwar Adadin Tafiye-tafiye Yayin Bikin Sharar Kaburbura Na Kasar Sin Na Bana
  • Tsohon Gwamnan Oyo, Omololu Olunloyo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 89
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
  • An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe
  • Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • ’Yansanda Sun Gayyaci Sanusi II Kan Kisan Jami’in Sa-kai Yayin Hawan Sallah A Kano
  • An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe
  • 2027: Tsananin Yunwa Zai Hana ‘Yan Nijeriya Sake Zaɓen Jam’iyyar APC – PDP