Gwamna Zamfara Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikata.
Published: 6th, March 2025 GMT
Gwamna Dauda Lawal ya amince da nadin Yakubu Sani Haidar a matsayin babban shugaban ma’aikatan jihar Zamfara.
Nadin wanda ke fara aiki nan take, ya fito ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar (SSG), Malam Abubakar Mohammad Nakwada, ta bakin babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Sulaiman Ahmad Tudu.
A cewar sanarwar, Haidar ya gaji Ahmad Liman, wanda ya yi ritaya a ranar 28 ga Fabrairu, 2025.
Haidar, wanda ya kammala karatunsa na kimiyyar siyasa a shekarar 1989 a Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, an nada shi Babban Sakatare a shekarar 2012, kuma ya yi aiki a ma’aikatu da hukumomi gwamnati da dai sauransu.
Gwamna Lawal ya bayyana godiya ga shugaban ma’aikata mai barin gado bisa sadaukarwar da ya yi wa jihar.
Ya bukaci sabon shugaban ma’aikatan da aka nada da ya kiyaye mutunci tare da bin ka’idojin aikin gwamnati wajen gudanar da ayyukansa.
REL/AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Amurka Ya Ce: Natenyahu Ba Zai Hadi Fada Da Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ba
Shugaban Amurka ya bayyana cewa: Fira ministan Isra’ila Netanyahu ba zai ja shi zuwa shiga cikin yaki da Iran ba, kuma a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci da shugaban kasar Iran
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya jaddada cewa: Ba za a sanya shi shiga yaki da Iran ba saboda manufofin fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu.
Trump ya kara da cewa a wata hira da ya yi da mujallar Time, a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci ko kuma shugaban kasar Iran.
Duk da imanin da ya yi cewa: Amurka da Iran za su iya cimma yarjejeniya, amma Trump ya sake nanata barazanarsa na cewa idan ba a cimma matsaya ba, to zai bi sahun ‘yan yahayoniyya wajen kai wa Iran hari, domin ganin cewa, Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.
Trump ya kuma musanta yunkurin cewa zai hana Isra’ila kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran.