Jam’iyyar PDP a jihar Gombe ta bayyana rashin jin dadin ta ga gwamna Inuwa Yahaya kan rabon kayan abinci da gwamnatin tarayya ta baiwa jihar a matsayin tallafin azumin watan Ramadan.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na jam’iyyar Abdulkadir Ahmad ya fitar a Gombe.

 

Jam’iyyar ta caccaki gwamnatin jihar kan rashin amincewa da rawar da gwamnatin tarayya ta taka, wanda hakan ya sanya ake yaudarar jama’a wajen ganin cewa tallafin na jiha ne kawai.

 

Jam’iyyar adawa ta ba da shawarar cewa yin shiru ya sa ayar tambaya game da gaskiya da rikon amana wajen tafiyar da kayayyakin agaji.

 

Ta kuma yi zargin cewa sukar da Gwamnan ya yi a baya game da ayyukan da gwamnatin tarayya ta yi, gami da rabon tireloli 20 na shinkafa a shekarar da ta gabata, na nuni da wani salon mayar da kokarin gwamnatin tarayya baya tare da sanya siyasa a rarraba kayan abinci.

COV HUDU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rabo gwamnatin tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

RAMADAN: Gwamnatin Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar 

 

Gwamna Umar Namadi ya amince da rage lokutan aiki ga ma’aikatan gwamnati a Jihar Jigawa yayin azumin Ramadan na 2025.

 

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar kuma aka rabawa manema labarai aDutse, wacce Babban Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ya sanya wa hannu.

 

“Farawa daga yanzu, ma’aikatan gwamnati a jihar za su rika fara aiki da karfe 9:00 na safe kuma su tashi da karfe 3:00 na yamma daga Litinin zuwa Alhamis, raguwar awanni biyu daga tsohon lokacin rufewa na karfe 5:00 na yamma. A ranakun Juma’a kuwa, ma’aikata za su fara aiki da karfe 9:00 na safe su kuma tashi da karfe 1:00 na rana, kamar yadda aka saba.” A cewar sanarwar.

 

Babban Sakataren ya bayyana cewa an yi hakan ne domin baiwa ma’aikatan gwamnati damar shiryawa azumin Ramadan da kuma gudanar da ibadu cikin sauki a wannan wata mai alfarma.

 

“An yi fatan cewa ma’aikatan gwamnati za su yi amfani da wannan lokaci don yin addu’o’i domin samun shiriya da albarka ga jiharmu,” in ji shi.

 

Alhaji Muhammad Dagaceri ya kara da cewa ana sa ran ma’aikatan za su yi amfani da lokacin azumi wajen yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki ga jihar da kasa baki daya.

 

END/ USMAN MZ

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsin Tattalin Arziki Ya Karfafa Mana Gwiwar Raba Tallafi Ramadan – Sarkin Fada
  • Gwamnatin Tarayya Ta Maka MultiChoice A Kotu Kan Karin Kuɗin DSTV Da GOtv
  • Wata Kotu A Iran Ta Ci Taran  Gwamnatin Amurka Dala Biliyon $12.6 Saboda Haddasa Mutuwar Masu Fama Da Cutar ‘thalassemia’ A Kasar
  • Babu abin da zai hana mu zama jam’iyya ɗaya da Kwankwaso — Shekarau
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar
  • Ramadan: Gwamnatin Jigawa ta rage lokacin aiki
  • RAMADAN: Gwamnatin Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar 
  • Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kano Cikin Shekara 1 – Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki