Sin Za Ta Kara Ingiza Samar Da Kudaden Gudanar Da Kamfanoni Masu Zaman Kansu
Published: 6th, March 2025 GMT
Shugaban hukuma mai lura da hada hadar samar da kudade ta kasar Sin Li Yunze, ya ce kasar za ta kara azamar samar da kudaden gudanar da kamfanoni masu zaman kan su, da kanana da mafiya kankantar sana’o’i.
Li, wanda ya yi tsokacin a Larabar nan, a gefen taron majalisar wakilan jama’ar kasar Sin dake gudana yanzu haka, ya ce Sin za ta kara yawan lamuni da ake baiwa sassa masu zaman kan su, da rage tsadar samar da kudaden sana’o’i, ta yadda hakan zai haifar da karin alfanu ga kamfanoni.
Jami’in ya kara da cewa, kamfanoni masu zaman kan su ne ke da kaso 92 bisa dari na jimillar kamfanonin dake kasar Sin, kuma akwai tarin hanayen jari a mafiya kankantar sana’o’i, da kananan kamfanonin dake kasar. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Yi Barazana Ga Ukraine A Dai-dai Lokacinda Ta Fitar Da Shirin Zaman Lafiya Da Rasha Na Karshe
Gwamnatin kasar Amurka ta gargadi kasar Ukraine a dai dai lokacinda ta gabatar da shirin zaman lafiya da kasar Rasha na karshe.
Shirin da shugaban kasar Donal Trump ya bayyana shi ne karshe dai, ya bukaci gwamnatin shugaba Volodimir Zelesky ta amince da yankin Cremea da kuma sauran yankunan hudu wadanda Rasha ta mamaye da karfi shekaru uku da suka gabata su zama mallakin kasar Rasha har’ abada. Sannan ta amince a daukewa kasar Rasha takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata tun bayan fara yakin. Sannan daga karshe ta amince ba zata shiga kungiyar tsaro ta NATO ba.
Shawara bata yi maganar wani abu banada wadannan hudu ba, duk da cewa Ukraine tana da wasu bukatu a yarjeniyar tsagaita wuta da kuma samar da sulhu mai dorewa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa Moscow ta bukaci a tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu don samun damar tattaunawa amma gwamnatin Kiev ta ki amincewa.
Masana suna ganin wadannan al-amura suna da nauyi ga kasar ta Ukraine, amma kuma bata da zabi tunda Amurka ce ta biya mafi yawan kudaden da Ukraine ta kashe a yankin.