Shugaban SWAN Ya Kafa Kwamatin Hadin Gwiwa Kan Harkar Zuba Jari
Published: 6th, March 2025 GMT
Shugaban kungiyar marubuta wasanni ta kasa SWAN, Kwamared Isaiah Benjamin, ya bukaci sabon kwamitin hadin gwiwar SWAN da aka kaddamar da su farfado da kungiyar ta hanyar jawo masu zuba jari don tallafa wa marubutan wasanni a fadin kasar nan.
Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin kwamred Isaiah Benjamin ya jaddada mahimmancin karfafa kudi ga ‘yan jaridun wasanni, yana mai baiwa kwamitin ‘yancin gudanar da aiki yadda ya kamata.
“Aikin da ke gaba yana da girma, amma ina da yakinin iya karfin ku na karfafa tattalin arzikin marubutan wasanni a Najeriya ta hanyar hadin kai. Kuna da cikakken goyon bayanmu, ”in ji shi.
Ya bayyana cewa zaben ‘yan kwamitin wanda shugaban kungiyar SWAN na jihar Nasarawa, Kwamared Smah George ya jagoranta ya dogara ne da irin nasarorin da suka samu da kuma gudunmawar da suke baiwa kungiyar.
Da yake mayar da martani a madadin kwamitin, Comrade Smah George ya nuna godiya ga hukumar zartaswa ta kasa bisa wannan dama da aka ba shi, ya kuma yi alkawarin yin aiki tukuru tare da masu ruwa da tsaki domin cika aikin kwamitin.
“Za mu bincika dukkan hanyoyin da ake da su don fitar da saka hannun jari a cikin SWAN. Ina kira ga mambobin kwamitin da su ci gaba da jajircewa kan wannan aiki domin yana da matukar muhimmanci wajen inganta walwala da kwanciyar hankali na marubutan wasanni,” inji shi.
Sabbin mambobin kwamitin da aka kaddamar sun hada da Ijeoma Peter Nwante mai wakiltar Kudu maso Gabas, Austin Ajayi arewa maso gabas, Clarkson Ogo Kudu maso Kudu, Bisi Ogunleye Kudu maso yamma, Hassan Abubakar arewa ta tsakiya da kuma Jacob Enjewo arewa maso yammat, wanda zai zama sakatare.
Aliyu Muraki/Lafia.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Lafiya nasarawa Wasanni
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Ce Yarjeniyar Tsagaita Wuta Ne Kadai Za Ta Kubutar Da Fursinonin Yahudawa Daga Hannun Kungiyar
Wani babban Jami’in kungiyar Hamas Osama Hamdan ya bayyana cewa hanya daya tilo ta kubutar da ragowar Fursinonin yahudawan HKI daga hannun kungiyar, kuma ita ce dabbaka bangare na 2 na yarjeniya tsagaita wuta tsakanin kungiyar da kuma HKI.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Osama Hamdan yana fadar haka a jiya Litinin. Ya kuma kara da cewa, akwai alamun Natanyahu Firai ministan HKI yana son ya sake komawa yaki a Gaza.
Hamdan ya ce, kafin haka gwamnatin HKI ta dakatar da aikin aiwatar da yarjeniyar da suka kulla da ita, yana son ya yi watsi da ita, sannan ya bukaci a sake tattaunawa kan sauran abubuwan da suka zo a cikin yarjeniyar.
Jami’in na Hamas y ace a bangare na farko na Yarjeniyar HKI ta sabawa yarjeniyar a wuraren da dama, kamar bukatar a tsawaita bangare na daya ko kuma a sake sabuwar tattaunawa.
Hamdan ya yi allawadai da saba wa yarjejeniyar ta 1, wacce ta hada wurare 210, daga ciki har da hana wadanda aka kora daga gidajensu komawa inda suka fito, kashe Falasdinawa 116, jinkiri wajen sakin Falasdinawan da aka yi musayarsu. Da kuma hana shigar kayakin agaji cikin Gaza.
HKI dai ta hana shigar kayakin agaji wanda bangare ne na yarjeniyar, da kayakin sake gina asbitoci da sauransu.