Shugaban kungiyar marubuta wasanni ta kasa SWAN, Kwamared Isaiah Benjamin, ya bukaci sabon kwamitin hadin gwiwar SWAN da aka kaddamar da su farfado da kungiyar ta hanyar jawo masu zuba jari don tallafa wa marubutan wasanni a fadin kasar nan.

 

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin kwamred Isaiah Benjamin ya jaddada mahimmancin karfafa kudi ga ‘yan jaridun wasanni, yana mai baiwa kwamitin ‘yancin gudanar da aiki yadda ya kamata.

 

“Aikin da ke gaba yana da girma, amma ina da yakinin iya karfin ku na karfafa tattalin arzikin marubutan wasanni a Najeriya ta hanyar hadin kai. Kuna da cikakken goyon bayanmu, ”in ji shi.

 

Ya bayyana cewa zaben ‘yan kwamitin wanda shugaban kungiyar SWAN na jihar Nasarawa, Kwamared Smah George ya jagoranta ya dogara ne da irin nasarorin da suka samu da kuma gudunmawar da suke baiwa kungiyar.

 

Da yake mayar da martani a madadin kwamitin, Comrade Smah George ya nuna godiya ga hukumar zartaswa ta kasa bisa wannan dama da aka ba shi, ya kuma yi alkawarin yin aiki tukuru tare da masu ruwa da tsaki domin cika aikin kwamitin.

 

“Za mu bincika dukkan hanyoyin da ake da su don fitar da saka hannun jari a cikin SWAN. Ina kira ga mambobin kwamitin da su ci gaba da jajircewa kan wannan aiki domin yana da matukar muhimmanci wajen inganta walwala da kwanciyar hankali na marubutan wasanni,” inji shi.

 

Sabbin mambobin kwamitin da aka kaddamar sun hada da Ijeoma Peter Nwante mai wakiltar Kudu maso Gabas, Austin Ajayi arewa maso gabas, Clarkson Ogo Kudu maso Kudu, Bisi Ogunleye Kudu maso yamma, Hassan Abubakar arewa ta tsakiya da kuma Jacob Enjewo arewa maso yammat, wanda zai zama sakatare.

 

Aliyu Muraki/Lafia.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiya nasarawa Wasanni

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin Tsakiyar JKS Ya Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Sakamakon Jawo Jarin Waje A Rubu’in Farko Na Bana Ya Ba Da Sha’awa A Kasar Sin
  • Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo
  • Wace Kungiya Ce Za Ta Lashe Kofin Zakarun Turai?
  • Na shiga fim ne don isar da saƙon Musulunci — Malam Inuwa Ilyasu
  •  Kotun Tsarin Mulki Ta Gabon Ta Tabbatar Da Nasarar Nguema A Zaben Shugaban Kasa
  • Kwamitin Tsakiyar JKS Ya Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki
  • An Bude Taron Dandalin Tattaunawar Afirka Ta Yamma Karo Na Farko A Senegal
  • Muna Farin Ciki Da Karramawar Da Gwamna Abba Ke Samu Saboda Aiki Tukuru – Hon. Ibrahim
  • Dattawan Arewa Sun Zargi Tinubu Da Nuna Wariya A Nade-Naden Mukamai
  • Gwamnan Kano ya kafa sabbin hukumomi 4