Rasha Ta Kai Hari Mahaifar Shugaban Ukraine Zelensky
Published: 6th, March 2025 GMT
Jami’ai a Ukraine sun ce mutane huɗu sun mutu, 29 da suka jikkata, a wani harin makami mai Linzami da Rasha ta kai kan wani Otel a birnin Kryvyi Rih – Mahaifar shugaba Zelensky.
Masu aikin ceto na ƙoƙarin zaƙulo masu sauran numfashi a ɓaraguzan gine-gine.
Wannan hari na zuwa ne sa’o’i bayan Amurka ta tabbatar da cewa ta daina musayar bayanan sirri da Ukraine — wanda haka zai kasance ƙalubale matuƙa ga Ukraine wajen iya daƙile hare-haren Rasha.
Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce masu aikin sa kai daga wata ƙungiyar bayar da agaji daga Amurka da Birtaniya na daga cikin waɗanda harin ya rutsa da su a daren jiya.
Hakazalika, an kai wasu hare-haren birnin Odesa wanda ya yi sanadiyyar jikkata mutum biyu da lalata manyan gine-gine biyu, kamar yadda gwamnan yankin, Oleh Kiper ya tabbatar.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno
Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari kauyen Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno, inda suka kashe sojoji tare da rasa mayaƙansu da dama.
Rahotanni na cewa harin ya auke ne da misalin karfe 1:00 na ranar Lahadi a lokacin da ’yan ta’addan suka mamaye sansanin sojin Nijeriya da ke garin Izge.
Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back An sayar da kare mafi tsada a duniyaWata majiyar tsaro ta tabbatar wa Aminiya cewar wani soji mai muƙamin Kyaftin da kuma Kofur na daga cikin waɗanda suka kwanta dama, yayin da sojoji suka yi nasarar hallaka mahara da dama a yayin arangamar.
Shugaban ƙaramar Hukumar Gwoza, Hon. Abba Kawu Idrissa Timta, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Sai dai ya ce har yanzu lokacin da aka tuntuɓe shi ba a kai ga tantance irin asarar da rayuka daga ɓangarorin biyu ba.
“Sai dai muna tabbatar da kashe ’yan ta’adda da dama,” a cewarsa.
Bayanai sun ce mahara da dama haye a kan babura sun mamaye sansanin sojojin, bayan da suka harba makamin roka da ake kira RPG a kansu.
Rahotanni sun ce, da farko sun kama hanyar nasara a kan sojoji, sai daga bisani mafarauta da ’yan banga suka ƙara ƙwarin guiwa har ta kai ga fatattakar maharan.
Majiyoyi sun ce sojoji da mafarauta da jajirtattun mazauna garin ne suka fatattaki ’yan ta’addan da ke tserewa zuwa dajin Sambisa.