Liverpool na farautar Kerkez, Real Madrid na son Konate
Published: 6th, March 2025 GMT
Liverpool na farautar ɗan wasan Bournemouth mai shekara 21 daga Hungary Milos Kerkez kan fam miliyan 40. (Telegraph – subscription required)
West Ham na kokarin ganin ta saye ɗan wasan tsakiya a Ingila, Angel Gomes mai shekara 24 daga Lille a sabuwar kaka. (Guardian)
Manchester United na tunanin ɗauko mai tsaron raga a Burnley, James Trafford mai shekara 22 ko kuma Joan Garcia mai shekara 23 daga Sifaniya, domin maye gurbin Andre Onana mai shekara 28 na Kamaru.
Real Madrid na son ɗan wasan Liverpool mai shekara 25 daga Faransa, Ibrahima Konate. (Mail – subscription required)
Real ta kuma nuna matsuwa kan ɗan wasan Bournemouth mai shekara 19 daga Sifaniya, Dean Huijsen, wanda cikin yarjejeniyarsa ake iya biyan fam miliyan 50 domin sayensa ga wata ƙungiya. (Talksport)
Barcelona na duba yiwuwar mallake ɗan wasan Newcastle mai shekara 27 daga Brazil, Bruno Guimaraes, wanda ƙungiyoyin Arsenal da Manchester City ke zawarci. (CaughtOffside)
Ɗan wasan tsakiya a Bayern Munich da Jamus, Joshua Kimmich mai shekara 30 na son zuwa Arsenal, yayinda ita ma Paris St-Germain ke nuna zawarcinta. (Bild – in German)
Ɗan wasan Manchester United da Brazil, Antony mai shekara 25, ya nuna sha’awar cigaba da zama a Real Betis idan yarjejeniyar zaman aronsa ta kawo karshe a ƙungiyar ta La Liga club. (Canal Sur, via Mail)
Liverpool ta kasance ƙungiya ta baya-bayanan da ke zawarcin ɗan wasan RB Leipzig, Benjamin Sesko mai shekara 21 daga Slovenia wanda burinsa ya je Landan, sannan Arsenal da Chelsea na bibbiyarsa. (TBR Football)
Tottenham na iya rabuwa da ɗan wasan Mali, Yves Bissouma mai shekara 28 a wannan kaka, yayinda take kokarin sake garambawul a tawagarta. (Football Insider)
West Ham ta tuntubi ɗan wasan Roma mai shekara 27 da Ingila,Tammy Abraham, da yanzu haka ke zaman aro a AC Milan. (Teamtalk)
Newcastle na duba yiwuwar saye ɗan wasan Fiorentina, mai shekara 25 daga Italiya, Moise Kean. (GiveMesport), external
Everton za ta bada damar sake daidatawa kan ɗan wasan Brazil, Richarlison mai shekara 27 daga Tottenham. (TBR Football)
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Wasanni mai shekara
এছাড়াও পড়ুন:
Mutanen Afrika Sun Kori Kasar Faransa Daga Kashensu Ne Saboda Ta Ki Ta Amince Da Yencinsu
Pierre de Gaulle, dan tsohon shugaban kasar Faransa Charles de Gaulle, wanda ya jagoranci kasar Faransa a samun yencin kasar daga hannun sojojin NAZi a yakin duniya na biyu, ya bayyana cewa kasashen Afrika sun kore kasar Faransa daga kasashensu ne bayan da kasar ta kasa yin abinda zai kawo ci gaban kasashen.
Kamfanin dillancin labaran Spunik na kasar Rasha ya nakalto jikan de Gaulle yace tsarin kasar Faransa na tattalin arziki da siyasa sun sanya kasashen cikin talauci da rashin ci gaba. Wannan ya sa suka zabi korar kasar Faransa daga kasashensu.