A Kasar Sudan Ta Kudu Jami’an Tsaro Sun Killace Gidan Mataimakin Shugaban Kasa
Published: 6th, March 2025 GMT
Kamfanin dillancin Labarun “Resuters” ya nakalto cewa jami’an tsaro sun killace gidan mataimakin shugaban kasa da wasu manyan jami’an soja da fararen hula.
Baya ga mataimakin shugaban kasa Riek Machar da sojoji su ka yi wa daurin talala a cikin gidansa, an kuma kama mataimakin hafsan hafsoshin sojan kasar Jamar Gabriel Doup Lam, sai kuma ministan man fetur Pout Kang Chol, haka nan kuma iyalansa da masu gadinsa.
Har ila yau a jiya Laraba an ga jami’an tsaro masu yawa sun killace ofishin mataimakin shugaban kasar, sai dai kuma wata majiyar ta ce, an gan shi ya isa wajen aikin nashi da safiyar jiya Laraba.
Wadannan matakan na tsaro dai sun biyo bayan fada mai tsanani da aka yi ne a tsakanin sojojin gwamnatin da kuma mayakan kabilar Nuwairah wacce mataimakin babban hafsan hafsoshin sojan kasar ya fito daga cikinta.
Gwamnatin shugaba Silva Kir tana tuhumar janar Doup Lam da cewa yana da hannu a tawayen ‘yan kalbilar tashi.
An sami asrar rayuka masu yawa a wannan fadan a tsakanin bangarorin biyu.
Shugaba Silva ya yi alkawalin cewa kasar ba za ta sake komawa cikin yaki ba.
A 2013 ne dai kasar ta Sudan Ta Kudu ta tsunduma cikin yakin basasa wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutanen da sun kai 400,000 da kuma mayar da mutane miliyan 2.5 zama ‘yan gudun hijira.
Jumillar mutanen kasar da sun kai miliyan 11 suna fafutukar samun abinci da kuma ruwan sha mai tsafta. Sai dai daga baya na yi sulhu a tsakanin bangarorin biyu na shugaba Silva Kir da kuma mataimakinsa Riek Machar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shari’ar ‘Yan Hamayyar Siyasa 40 A Tunisiya Ya Jefa Kasar Cikin Takaddama
Kasar Tunisiya ta shiga cikin sabuwar dambaruwar siyasa saboda yadda ake yi wa wasu fitattun ‘yan siyasa, lauyoyi da kuma ‘yan jarida 40 shari’a, bisa zargin cewa suna yi wa kasa makarkashiya.
An jibge jami’an tsaro masu yawan gaske a bakin kotun, yayin da a wajenta kuma masu fafutuka suke bayar da taken nuna kin amincewa da shari’ar, suna bayar da taken; ‘Neman ‘ ‘yanci, da kuma zargin ma’aikatar shari’a da zama ‘yar koren gwamnati.
Lauya a cikin kwamitin lauyoyi masu bayar da kariya ga wadanda ake yi wa shari’ar, Lamia Farhani ta bayyana cewa; Abin ban mamaki shi ne shugaban kasa wanda ya rantse zai kare shari’a, wanda kuma shi kwararre ne akan tsarin mulki shi ne na farkon da ya karya doka.
Wani daga cikin ‘yan kasa da su ka halarci gangamin mai suna Ahlem ya shaida wa kamfanin dillancin labaurn “Associated Press” cewa; Ya zo ne domin ya nuna goyon bayansa ga wadanda ake tsare da su, tare da tuhumar gwamnatin kasar da cewa garkuwa take yi da mutanen da take yi wa shari’a.
Sai dai kuma wasu ‘yan kasa suna da ra’ayin da yake cin karo da wannan, suna ganin cewa wadanda ake yi wa shari’an sun cancanci a daure su tsawon rai. Har ila yau ya kuma tuhumi ‘yan siyasar da ake yi wa shari’ar da cewa, sun ruguza tattalin arzikin kasar ta yadda darajar kudaden kasar ta fadi kasa.
A gefe daya MDD ta yi kira ga gwamntin ta Tunisiya da ta kawo karshen duk wata shari’a ta siyasa da ake yi wa ‘yan hamayya, sannan kuma ta bar mutanen kasar cikin ‘yancin bayayna ra’ayoyinsu.
MDD ta ce, yi wa ‘yan hamayyar shari’a zai mayar da tsarin demokradiyyar kasar baya.