HausaTv:
2025-04-26@13:50:00 GMT

Shari’ar ‘Yan Hamayyar Siyasa 40 A Tunisiya Ya Jefa Kasar Cikin Takaddama

Published: 6th, March 2025 GMT

Kasar Tunisiya ta shiga cikin sabuwar dambaruwar siyasa saboda yadda ake yi wa wasu fitattun ‘yan siyasa, lauyoyi da kuma ‘yan jarida 40 shari’a, bisa zargin cewa suna yi wa kasa makarkashiya.

An jibge jami’an tsaro masu yawan gaske a bakin kotun, yayin da a wajenta kuma masu fafutuka suke bayar da taken nuna kin amincewa da shari’ar, suna bayar da taken; ‘Neman ‘ ‘yanci, da kuma zargin ma’aikatar shari’a da zama ‘yar koren gwamnati.

Lauya a cikin kwamitin lauyoyi masu bayar da kariya ga wadanda ake yi wa shari’ar, Lamia Farhani ta bayyana cewa; Abin ban mamaki shi ne shugaban kasa wanda ya rantse zai kare shari’a, wanda kuma shi kwararre ne akan tsarin mulki shi ne na farkon da ya karya doka.

Wani daga cikin ‘yan kasa da su ka halarci gangamin mai suna Ahlem ya shaida wa kamfanin dillancin labaurn “Associated Press” cewa; Ya zo ne domin ya nuna goyon bayansa ga wadanda ake tsare da su, tare da tuhumar gwamnatin kasar da cewa garkuwa take yi da mutanen da take yi wa shari’a.

Sai dai kuma wasu ‘yan kasa suna da ra’ayin da yake cin karo da  wannan, suna ganin cewa wadanda ake yi wa shari’an sun cancanci a daure su tsawon rai. Har ila yau ya kuma tuhumi ‘yan siyasar da ake yi wa shari’ar da cewa, sun ruguza tattalin arzikin kasar ta yadda darajar  kudaden kasar  ta fadi kasa.

A gefe daya MDD ta yi kira ga gwamntin ta Tunisiya da ta kawo karshen duk wata shari’a  ta siyasa da ake yi wa ‘yan hamayya, sannan kuma ta bar mutanen kasar cikin ‘yancin bayayna ra’ayoyinsu.

MDD ta ce, yi wa ‘yan hamayyar shari’a zai mayar da tsarin demokradiyyar kasar baya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ake yi wa shari yi wa shari a da ake yi wa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojan HKI Ya Halaka A Gaza

Kafafen watsa labarun HKi sun amabci cewa daya daga cikin sojojinsu ya halaka a Gaza, yayin da wasu 7 su ka jikkata.

Kafafen watsa labarun na HKI sun ce, Harin da aka kai wa sojojin ya kunshi harbi daga kwararren maharbi da kuma harba makamin dake fasa motoci masu sulke.

An ga jiragen sojan mamaya suna tsananta hare-hare a yankin da lamarin ya faru, saboda su sami damar dauki gawar sojan nasu da kuma wadanda su ka jikkata.

Tashar talabijin ta 12; ta HKI ta ambaci cewa;Ana gwabza fada ne a arewacin Gaza, kuma mazauna yankin suna cewa sun ga jiragen sama masu yawa suna kai da komo.

 Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare masu yawa a yankin Arewacin Gaza, kamar kuma yadda wata kafar ta ce an ji karar fashewar wasu abubuwa da karfi a cikin yankin Naqab ta yamma.

A wani labarin daga Gaza, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada a yau kadai sun kai 56.

Jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a yankunan Arewan yammacin Gaza da kuma Jabaliya da shi ne musabbabin shahadar adadi mai yaw ana Falasdinawan a yau.

A Jabaliya kadai jiragen yakin HKI sun kai hari ne akan wani gida da ‘yan hijira suke cikinsa, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 15.

A Arewacin Gaza kuwa mutane an sami shahidai 39, sai kuma wasu 7 da su ka jikkata a cikin birnin Gaza kamar yadda kamfanin dillancin labarun “Anatoli” ta Turkiya ya nakalto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake
  • ’Yar Arewa da ta kafa tarihin samun Digiri Mai Daraja ta ɗaya a fannin Shari’a
  • Sayyid Fadhlullahi Ya Jaddada Muhimmanci Samar Da Makamai Ciki Har Da Kare Kasa Daga Dan Mamaya
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  •  Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi
  • IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya
  • Arakci: Mun Yi Tattaunawa Mai Kyau Da Mahukuntan Kasar China