Sojoji Sun Kashe Ƙwararren Mai Haɗa Wa Boko Haram Bam A Borno
Published: 6th, March 2025 GMT
Sojojin sun kuma ƙwato makamai masu yawa.
Bayan artabun, Boko Haram sun yi yunƙurin kai farmakin ramuwar gayya ta hanyar birne bama-bamai a hanyoyin da sojojin za su bi.
Sai dai dakarun sun gano sama da guda 10 daga cikin abubuwan fashewar kuma sun tarwatsa su, wanda hakan ya hana aukuwar asarar rayuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Boko Haram Dakaru
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
An garzaya da ita asibitin Misau, daga nan aka mayar da ita zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Azare, inda aka tabbatar da mutuwarta.
Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi, CSP Ahmed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis.
Ya ce waɗanda aka kama sun amsa laifin kuma sun bayyana sunayen wasu da suka haɗa kai da su.
Cikin sauran waɗanda aka kama har da Alkali Kawu, Maule Mai Ride, Mai Tumatir, Danguli, Yakubu da Kura.
Wakil ya ce bincike yana guduna a hedikwatar ‘yansanda ta Misau, kuma sun ƙudiri aniyar ganin adalci ya tabbata.
Ya ƙara da cewa bayan kammala bincike, za a gurfanar da su a gaban kotu domin fuskantar hukunci daidai da laifin da suka aikata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp