Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ, FRCN Kaduna Chapel, ta jaddada kudirinta na inganta jin dadin mambobinta ta hanyar bullo da sabbin tsare-tsare da shirye-shiryen tallafi.

Shugaban kungiyar, Kwamared Umar Adamu Sarikin Fada ne ya bayyana haka a lokacin rabon kayan abinci na Ramadan ga ‘yan kungiyar a Kaduna.

Umar Adamu Sarikin Fada ya bayyana cewa shirin rabon kayayyakin na daga cikin dabarun da kungiyar ta keyi na dakile tasirin tabarbarewar tattalin arzikin kasar nan.

Ya tabbatar da cewa sama da ‘yan uwa Musulmi dari da hamsin ne suka ci gajiyar shirin na watan Ramadan na bana, inda ya jaddada cewa su ma Kirista na kungiyar sun samu irin wannan tallafi a lokacin bukukuwan Kirsimeti na 2024.

Shugaban ya kuma yi kira ga mambobin kungiyar da su sake sadaukar da kansu wajen gudanar da ayyukansu domin ci gaban FRCN da kasa baki daya.

REL/MANSUR S PAKI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Raba Tallafin Ramadan A Mazabarsa

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Yusuf Dahiru Liman, ya raba kayayyakin agaji na watan Ramadan na sama da Naira miliyan 200 ga al’ummar mazabarsa.

Ya yi hakan ne da nufin tallafa wa al’umma domin samun damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki, duba da halin da ake ciki na tabarbarewar tattalin arziki.

A wajen bikin kaddamar da rabon, Yusuf Dahiru Liman, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan ofishinsa, Bashir Adamu Nababa, ya jaddada aniyarsa ta rage wahalhalun da al’ummar mazabarsa ke fuskanta.

Ya bayyana rabon kayayyakin a matsayin wani bangare na alkawarin da ya dauka na inganta walwalar jama’a a yayin  yakin neman zabe.

Shugaban kwamitin masu ruwa da tsaki, Isiyaku Adamu Nababa, ya jaddada cewa shirin ya nuna irin sadaukarwar da shugaban majalisar yake yi na yi wa al’ummarsa hidima baya ga  ayyukan majalisa.

Ya bayyana sauran ayyukan jin kai da Yusuf Liman ya jagoranta, da suka hada da ayyuka a fannin ilimi, da  kiwon lafiya, da kuma sanin makamar aiki.

Da yake jawabi a wajen taron, Hakimin Barnawa, Alhaji Kabiru Zubairu, ya bayyana jin dadinsa bisa jajircewar da kakakin majalisar ya yi wajen kyautata rayuwar al’ummar mazabarsa.

Ya yaba da yadda shugaban majalisar ke gudanar da jagoranci, wanda ke tafiya da kowa ba tare da  bambancin addini ko kabila ba.

Shi ma mataimakin shugaban Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, Nehemiah Baba Karik, ya yaba da yadda Shugaban Majalisar yake aiki ba tare da nuna son kai ba, inda ya ce yana yi wa dukkan mazauna yankin hidima bisa adalci.

A nasa jawabin,  Shugaban Majalisar Limamai da Malamai na mazabar Makera Malam Ibrahim Mahe, ya yaba da wannan karamci, inda ya ce ya zo a daidai lokacin da dace.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya sakawa shugaban majalisar bisa kokarinsa na tallafawa al’ummar jihar Kaduna.

Wadanda suka ci gajiyar wannan karimcin sun hada da malamai maza da mata na makarantun islamiyya, da manyan limamai, da  kungiyoyin Nisa’us Sunnah na Barnawa, da Makera, da Kakuri, da masu rike da  sarautun gargajiya, da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC, da sauransu.

Sauran sun hada da hukumomin tsaro da suka hada da rundunar sa kai ta  Civilian JTF, da kuma kungiyoyin agaji na  JIBWIS, da  Fityanul Islam, da Jama’atu Nasril Islam da dai sauransu.

Da dama daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin sun nuna matukar godiya ga wannan karamcin, inda suka yi addu’o’in Allah ya ci gaba da yi ma shugaban majalisar jagoranci da samun nasara a ayyukansa.

 

Shamsuddeen Mannir Atiku

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • PDP Ta Caccaki Gwamnan Gombe Saboda Rabon Tallafin Abinci….
  • Ramadan: Gwamnatin Sakkwato Ta Rage Wa Ma’aikata Lokacin Aiki
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Raba Tallafin Ramadan A Mazabarsa
  • Iran Ta Ce Dole Ne Amurka Ta Janye Mata Takunkuman Tattalin Arziki Masu Gurgurtawa Da Ta Dora Mata
  • Kasafin Kuɗin 2025 Taswira Ce Ta ƙarfafa Tattalin Arziki Da Ci Gaban ƙasa – Ministan Yaɗa Labarai
  • Ramadan: Gwamnatin Jigawa ta rage lokacin aiki
  • Kasafin Kudin Bana Zai Samarda Tsarin Tattalin Arziki Da Cigaban Ƙasa: Ministan Labarai
  • Ba Za Mu Tattauna da Rasha Ba Sai Ta Daina Kai Mana Hari – Zelensky
  • Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki