Aminiya:
2025-04-26@08:00:21 GMT

Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6

Published: 6th, March 2025 GMT

Kwamitin Majalisar Dattawa ya bayar da shawarar a dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, na tsawon watanni shida.

Kwamitin ladabtarwa da ɗa’a ne, ya bayar da shawarar biyo bayan zargin da ta yi wa Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, kan cin zarafinta.

Sheikh Sa’idu Hassan Jingir ya rasu A yi adalci a binciken mutuwar dan kwallon Nijerirya a Uganda —Gwamnatin Sakkwato

A zaman Majalisar Dattawa na ranar Alhamis, Shugaban kwamitin, Neda Imasuen, ya gabatar da rahoton kwamitin, inda ya bayyana cewa Natasha ta ƙi bayar da haɗin kai wajen binciken da aka yi.

Kwamitin ya kuma bayar da shawarar a dakatar da biyanta albashi tare da janye mata jami’an tsaron da ke kula da ita.

Rikicin ya fara ne bayan da Sanata Natasha ta zargi Akpabio da ƙin amincewa da wasu ƙudurorinta, musamman wanda ya shafi Kamfanin Ƙarafa na Ajaokuta.

Haka kuma, ta ce Akpabio ya kira ta da suna “yar kulob” a zaman Majalisar, kodayake daga baya ya ba ta haƙuri.

A martaninsa, Akpabio ya musanta dukkanin zarge-zargen, inda ya bayyana cewa yana girmama mata kuma bai aikata wani abin da bai dace ba.

Wasu Sanatoci sun samu bambancin ra’ayi game da hukuncin dakatarwar.

Sanata Abba Moro daga Benuwe ta Kudu, ya bayar da shawarar a rage wa’adin dakatarwar zuwa watanni uku kawai, yayin da wasu ke goyon bayan hukuncin watanni shida.

Yanzu Majalisar Dattawa za ta tattauna kan rahoton kwamitin domin yanke hukunci na ƙarshe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi dakatarwa Kwamiti Majalisar Dattawa zargi Majalisar Dattawa

এছাড়াও পড়ুন:

IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya

Asusun bayar da lamuni na duniya ( IMF) ya yi gargadin cewa rashin tabbataci da Karin kudin harajin Amurka ya haddasa zai iya kawo tsaiko a cikin harkokin cinikiyya ta duniya.

Sanarwar wacce babban jami’in ttatalin arziki na Asusun bayar da lamunin na duniya Pierre -Oliver-Gourinchas, ya bayyana ta kara da cewa; Za a iya samun karuwar hargitsi a cikin harkokin tattalin arzikin na duniya da dama yake fama da matsala.

Jami’in ya yi bayani ne  bayan sake yin hasashe akan ci gaban tattalin arzikin duniya, wanda aka fitar a cikin rahoto a ranar Talatar nan.

Asusun bayar da lamunin ya yi hasashen cewa tattalin arzikin duniyar zai bunkasa da kaso 2.8 % a cikin 2025, da hakan yake nuni da koma baya mai tsanani da ya kai 0.5, idan aka kwatantan da hasashen da ya yi a baya a watan Janairu.

Bayan da Amurka ta sanar da Karin kudaden fito akan kayan kasuwanci da ake shigar mata daga kasashen mabanbanta, cibiyoyin kudi na duniya sun yi hasashe, tare da nuni da cewa za a sami koma baya a ci gaban tattalin arzikin na duniya.

Rahoton ya kuma yi gargadi akan  dagula kasuwanci, da hakan zai iya haddasa tsaiko na ci gaba, ko ma haddasa sauyi a hada-hadar kudade.

 Asusun bayar da lamunin na duniya ya yi kira ga kasashe da su bude tattaunawa a tsakaninsu, su kuma samar da daidaito a cikin dokokin kasuwanci, da kiyaye ‘yancin da hada-hadar kudade suke da shi, saboda karfafa tattalin arzikin duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamitin Tsakiyar JKS Ya Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki
  • Hajji 2025: Hukumar Alhazan Yobe ta gudanar da taro don mahajjata
  • Amurka Ta Yi Barazana Ga Ukraine A Dai-dai Lokacinda Ta Fitar Da Shirin Zaman Lafiya Da Rasha Na Karshe
  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shirin Tsaftar Muhalli Na Wata Wata Saboda Jarrabawar JAMB
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Nada Amirul Hajj Bana
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • Shawarar Tabbatar Da Tsaro A Duniya Ta Samar Da “Kyakkyawan Fata” Ga Duniya Mai Fama Da Tashin Hankali
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  • IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya
  • Rohoton Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Ya Tabbatar Da Tafka Manyan Laifukan Cin Zarafin Bil-Adama A Siriya