Ƴar Majalisar Dattawa Natasha Akpoti Na Fuskantar Dakatarwar Wata Shida
Published: 6th, March 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya dage dakatarwar da aka yi wa mai bashi shawara na musamman kan harkokin albashi da fansho, Bashir Ado Kazaure da aka mishi a baya ba tare da bata lokaci ba.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Jigawa Malam Bala Ibrahim ya sanyawa hannu kuma ya bai wa manema labarai.
Sanarwar ta bayyana cewa, matakin na zuwa ne bayan wani kwakkwaran bincike da kwamitin da aka kafa karkashin jagorancin babban lauyan gwamnati kuma kwamishinan shari’a na jihar Barista Bello Abdulkadir Fanini ya gudanar.
“Rahoton kwamitin ya yi tsokaci kan al’amuran da suka dabaibaye dakatarwar da aka yi wa Bashir Kazaure, biyo bayan sanarwar batun biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 kafin lokacin da gwamnati ta shirya sanarwa a hukumance,” in ji shi.
Sakataren gwamnatin jihar ya bayyana cewa, matakin dage dakatarwar na nuni da yadda Gwamnan ya jajirce wajen tabbatar da adalci da bin doka da oda wajen tafiyar da al’amura.
Usman Muhammad Zaria