Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya dage dakatarwar da aka yi wa mai bashi shawara na musamman kan harkokin albashi da fansho, Bashir Ado Kazaure da aka mishi a baya ba tare da bata lokaci ba.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Jigawa Malam Bala Ibrahim ya sanyawa hannu kuma ya bai wa manema labarai.

Sanarwar ta bayyana cewa, matakin na zuwa ne bayan wani kwakkwaran bincike da kwamitin da aka kafa karkashin jagorancin babban lauyan gwamnati kuma kwamishinan shari’a na jihar Barista Bello Abdulkadir Fanini ya gudanar.

“Rahoton kwamitin ya yi tsokaci kan al’amuran da suka dabaibaye dakatarwar da aka yi wa Bashir Kazaure, biyo bayan sanarwar  batun biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 kafin lokacin da gwamnati ta shirya sanarwa a hukumance,” in ji shi.

Sakataren gwamnatin jihar ya bayyana cewa, matakin dage dakatarwar na nuni da yadda Gwamnan ya jajirce wajen tabbatar da adalci da bin doka da oda wajen tafiyar da al’amura.

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Natasha Na tsawon Watanni 6 Saboda Rashin Da’a
  • Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na Watanni 6
  • Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6
  • Kwamitin Majalisa Ya Yi Watsi Da Ƙorafin Da Natasha Ta Shigar A Kan Akpabio
  • Natasha Da Akpabio: Sanata Natasha Ta Gabatar Wa Majalisar Dattawa Ƙorafinta
  • An Koya Min Girmama Mata – Akpabio Ya Musanta Zargin Cin Zarafin Natasha
  • Majalisar Dattawa Ta Ki Amincewa Da Tattaunawar Kai Tsaye Da Natasha A Gaban Kwamitin Majalisar 
  • Dalilin da ba za mu binciki Akpabio kan zargin cin zarafin Natasha ba — Majalisar Dattawa