Leadership News Hausa:
2025-03-06@18:17:00 GMT

Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe Su 

Published: 6th, March 2025 GMT

Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe Su 

Jami’an hukumar yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi ta NDLEA a Kano sun shiga hannu bayan sun harbe wata budurwa mai shekaru 19, Patience Samuel, a unguwar Jaba.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:55 na dare a ranar Laraba, inda rahotanni suka nuna cewa jami’an ‘yansanda sun kai ɗauki, suka kwashe ta zuwa Asibitin koyarwa na Abdullahi Wase, inda aka tabbatar da rasuwarta.

NDLEA Ta Kama Tsoho Mai Shekaru 75 Da Dillancin Ƙwayoyi A Kano Kotu Ta Ɗaure ‘Yan Tiktok 2 Kan Yaɗa Kalaman Batsa A Kano

An kama jami’an biyu, Nass Ridwan Usman mai shekaru 23 da Ismaila Yakubu mai shekaru 26, waɗanda ke aiki a shalƙwatar NDLEA a Kano.

Har yanzu NDLEA ko ‘yansanda ba su fitar da wata sanarwa dangane da lamarin ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaliban Jami’ar Binuwe Da Aka Sace Sun Sami Ƴanci

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗaliban Jami’ar Binuwe Da Aka Sace Sun Sami Ƴanci
  • An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Binuwai
  • A Kasar Sudan Ta Kudu  Jami’an Tsaro Sun Killace Gidan Mataimakin Shugaban Kasa
  • Wata Kungiya Mai Zaman Kanta Ta Ba Masu Bukata Ta Musamman Su 450 Tallafi a Kano
  • Trump Ya Yi Barazanar Korar Daliban Da Ke Goyon Bayan Falasdinawa
  • Majalisar Zartarwa Ta Tarayyar Najeriya Ta Amince Da Kirkirar Sabbin Jami’oi 11
  • ‘Yan Fashi Da Makami Sun Kashe Tsohon Babban Kwanturolan Hukumar NIS A Abuja 
  • Jami’an tsaro sun hana jama’a kwasar mai bayan hatsarin tanka a Taraba
  • NDLEA ta cafke madugun fataucin miyagun ƙwayoyi bayan shekaru 17 yana ɓuya