Aminiya:
2025-04-08@13:51:28 GMT

Gwamnatin Ogun ta rufe kamfanoni saboda mutuwar ma’aikata

Published: 6th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Ogun ta rufe masana’antu guda biyu, na Quantum Steel Industry da ke Ogijo, a Ƙaramar Hukumar Sagamu da kuma kamfanin Xinfeng Plastics Limited da ke kan hanyar Legas zuwa Ibadan.

An rufe kamfanonin sakamakon haɗurran da ake samu a masana’antun da suka yi sanadin asarar rayuka.

An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Binuwai An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna

An rufe kamfanin Quantum Steels saboda fashewar wani abu da ya raunata wasu ‘yan Najeriya bakwai da ma’aikata ‘yan ƙasashen waje.

Haka kuma an rufe kamfanin Xinfeng Plastics bayan da wani ma’aikacin na’ura mai suna Ishaku Monday ya rasa ransa sakamakon wutar lantarki.

Mai baiwa gwamna shawara na musamman kan Hukumar kare muhalli ta Jihar Ogun, OGEPA wanda kuma shi ne yake riƙe da matsayin shugaban kwamitin yaƙi da muhalli na jihar, Farook Akintunde ya ce gwamnati ta ɗauki matakin rufe kamfanonin ne domin gudanar da bincike kan musabbabin aukuwar lamarin cikin gaggawa da kuma samar da mafita don daƙile afkuwar lamarin nan gaba.

“A matakin gwamnati, mun ƙuduri aniyar gudanar da sahihin bincike tare da gayyato masana harkokin tsaro na waje domin gano musabbabin faruwar wannan lamari domin kare lafiyar jama’a.

“Abin da ya fi muni shi ne, duk da ziyarar da gwamnatin jihar ke kai wa waɗannan kamfanoni a kai-a kai kamar yadda sauran jihohin ke yi don wayar da kansu kan buƙatar bin ƙa’idojin tsaro, irin waɗannan al’amura sun faru a cikin gudanar da harkokin kamfanin da suke samar da su wanda ya yi sanadin asarar rayuka, don haka akwai buƙatar a rufe su,” in ji shi.

Akintunde ya ƙara da cewa kamfanonin biyu za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai an kammala bincike tare da kafa sababbin ƙa’idojin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Quantum Steel Industry

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta daure ango wata 6 saboda likin kudi a bikinsa

Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kano ta yanke wa wani shahararren mai sana’ar gyaran fuska, Abdullahi Musa Huseini, wanda aka fi sani da Amuscap, hukuncin daurin watanni shida a gidan yari saboda yin likin da takardun Naira a lokacin bikin aurensa.

Mai Shari’a S.M. Shu’aibu ya yanke wa Huseini Amuscap hukuncin ne bayan ya amsa laifinsa da ake tuhumar sa, wanda ya saba wa sashe na 21(1) na Dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) ta shekarar 2007.

Takardar tuhumar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 6 ga Disamba, 2024, a Cibiyar Bikin Ali Jita da ke Kano, inda aka ga angon a wani bidiyo yana yin kari da Naira dubu dari a takardun Naira dubu daya-daya a yayin da yake rawa.

Bayan lauyan Hukumar Yaki da Masu Karya Tattalin Arziki Zagon Kasa (EFCC), Zarami Mohammed, ya gabatar da hujjojin karar tare da shaidar bidiyo a kotu. da kuma amsar laifin Huseini, Mai Shari’a Shuaibu ya ya yanke masa hukuncin daurin watanni shida a gidan yari ba tare da zabin tara ba.

Gaza: Isra’ila ta kashe Falasdinawa 58 a awa 58 Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu

Hukumar EFCC ta ci gaba da gargadin jama’a game da bata ko kuma yin amfani da takardun Naira ba daidai ba, musamman a lokacin bukukuwan jama’a, tana mai bayyana irin wadannan ayyukan a matsayin zagon kasa ga tattalin arziki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta daure ango wata 6 saboda likin kudi a bikinsa
  • Hafsan Soji Ya Gana Da Shugabanni A Filato Kan Hare-haren Da Suka Yi Ajalin Mutane
  • Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • HOTUNA: Yadda zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta gudana a wasu biranen Nijeriya
  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka 
  • HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas
  • ACF ta nemi Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen kisan jama’a a Filato
  • Hamas Ta Yaba Da Ma’aikaciyar Kamfanin Microsoft Wacce Ta Fallasa Yadda Kamfanin Yake Taimakawa HKI
  • Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025
  • ’Yan sanda sun gayyaci Sarki Sanusi domin amsa tambayoyi