Aminiya:
2025-03-06@18:04:27 GMT

Tsarin Sufuri: Gwamnatin Kano da kamfanin Stata sun ƙulla yarjejeniya

Published: 6th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kano, ta ƙulla yarjejeniya da kamfanin Stata Logistics Limited domin kafa sabon tsarin sufuri na zamani da za a dogara da amfani da CNG (Compressed Natural Gas) a jihar.

A taron da aka gudanar a Ma’aikatar Sufuri ta Kano, Daraktan Kamfanin Stata Logistics, Chuks Nwani, ya bayyana cewa shirin zai rage cunkoson ababen hawa a titunan Kano.

Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6 An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna

Hakan zai samu ne ta hanyar maye gurbin ƙananan motoci da sabbin bas-bas na zamani masu amfani da CNG.

Waɗannan bas-bas za su iya ɗaukar fasinjoji da kashi 120 sama da motocin sufuri na yanzu, wanda zai samar da tafiya mai sauƙi, aminci, da arha ga al’ummar Kano.

“Burinmu shi ne inganta sufuri a Kano ta hanyar amfani da CNG, wanda zai rage tsadar tafiye-tafiye da kuma saurin isa inda ake so idan aka kwatanta da tsarin yanzu,” in ji Nwani.

Sabbin Bas-Bas da Sabbin Tashoshin CNG

A wani ɓangare na shirin, kamfanin Stata Logistics zai gina tashoshin CNG guda shida a Kano don tabbatar da wadataccen gas ga motocin sufuri.

Haka nan, za a fara da saka jarin bas-bas 135, kowane na da darajar kusan dala 140,000, wanda gaba ɗaya zai kai dala miliyan 25.

“Muna buƙatar goyon bayan gwamnati ta hanyar samar da manufofin da za su tabbatar da nasarar wannan shiri, domin al’umma su amfana da tsarin sufuri na zamani,” in ji Nwani.

Goyon Bayan Gwamnatin Kano

Kwamishinan Sufuri na Kano, Ibrahim Ali Namadi, ya yaba da shirin, wanda ya dace da sabuwar dokar Kano Metropolitan Agency (KAMATA), wacce aka kafa domin tsara sufuri a Kano.

“Sun gabatar da kyakkyawan shiri don inganta sufuri a Kano, kuma mun ba su damar ci gaba da shirye-shiryen da suka dace.

“Bayan sun kammala, za mu gabatar da shirin ga Mai Girma Gwamna domin tantancewa,” in ji Namadi.

Ya ƙara da cewa yana da yaƙinin cewa wannan tsarin zai kawo ci gaba mai yawa, inda ya kafa misali da Jihar Legas a matsayin abin koyi a fannin gyaran tsarin sufuri na birane.

“Wannan ci gaba ne mai muhimmanci. Idan aka aiwatar da shi cikin nasara, Kano za ta zama birni na biyu mafi girma a Najeriya da ke da irin wannan tsarin sufuri na zamani,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin Kano Tsari tsarin sufuri na

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Libya Ta Kore Cewa Za Ta Karbi Bakuncin Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira

Gwamnatin hadin kan kasa dake yammacin Libya ta kore labarun da kafafen watsa labarun yammacin turai suke watsa na cewa, za ta karbi bakuncin Falasdinawa –akarkashin shirin Trump na korar mutanen Gaza.

Sanawar gwamnatin wacce ofishin shugabanta Abduhamid al-Dubaibah ya fitar ya bayyana cewa; Libya tana jaddada matsayarta akan cewa, hakkin Falasdinawa ne su rayu a cikin kasarsu.

Sanarwar da aka wallafa a shafin ‘facebook’ ta kuma ce; Wancan labarun na karya ne babu kamshin gaskiya a cikinsu, tare da bayyana wadanda su ka watsa su da cewa, ba su yi aiki da mafi karancin ka’ida ta aikin watsa labaru ba, kuma manufar ita ce wasa da hankalin mutane.

Haka nan kuma ta ce wanda ya rubuta rahoton Jerome Kersey ba kwararren dan jarida ba ne, mutum ne wanda ya shahara da watsa labarun karya ba tare da dogaro da wata hujja ba.

Bugu da kari bayanin ya sake jaddada matsayar Libya akan batun Falasdinu da kare hakkokinsu na su yi rayuwa a cikin mutunci a cikin kasarsu.

Tun a ranar 25 ga watan Janairu ne dai shugaban kasar Amurka Donald Trump yake magana akan  fitar da Falasdinawa daga Gaza zuwa kasashen makwabta kamar Masar da Jordan,lamarin da kasashen biyu su ka yi watsi da shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Ogun ta rufe kamfanoni saboda mutuwar ma’aikata
  • Wata Kungiya Mai Zaman Kanta Ta Ba Masu Bukata Ta Musamman Su 450 Tallafi a Kano
  • MDD Ta Nuna Cikakken Goyon Bayanta Ga Shirin Sake Gina Gaza Da Larabawa Su Ka Gabatar
  • Gwamnatin Libya Ta Kore Cewa Za Ta Karbi Bakuncin Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira
  • Kasafin Kudin Bana Zai Samarda Tsarin Tattalin Arziki Da Cigaban Ƙasa: Ministan Labarai
  • Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kano Cikin Shekara 1 – Gwamnatin Tarayya
  • Angola Zata Shiga Shirin ‘Yankunan Kasuwanci’ Na Kungiyar SADC
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD Ta Ce Sauye-Sauyen Da Ke Faruwa A Amurka Zai Shafi Al-Amura Da Dama A Majalisar
  • Masar : Za’a Gabatar Da Shirin Baiwa Falasdinawa Yancin Zama A Kasarsu