Aminiya:
2025-04-06@11:25:08 GMT

Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na Watanni 6

Published: 6th, March 2025 GMT

Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, na tsawon watanni shida.

Wannan hukunci ya biyo bayan amincewa da rahoton Kwamitin Ladabtarwa da Ɗa’a na Majalisar, wanda ya bincike ta kan zargin karya dokokin majalisar.

Tsarin Sufuri: Gwamnatin Kano da kamfanin Stata sun ƙulla yarjejeniya Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6

Sanata Natasha ta ƙi bayyana a gaban kwamitin a ranar Laraba, duk da gayyatar da aka yi mata domin ta kare kanta.

A sakamakon haka, majalisar ta yanke hukuncin dakatar da ita har na tsawon watanni shida.

’Yar majalisar ta shiga takun saƙa da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan rabon kujeru a zauren majalisar.

Haka kuma, Natasha ta zargi Akpabio da cin mutuncinta a bainar jama’a da kuma hana ta gabatar da ƙudirorinta a zauren majalisar.

Ƙin amincewarta da sabon tsarin rabon kujeru ya sa Shugaban Majalisar ya hana ta damar yin magana a zauren, wanda hakan ya haifar da saɓani a tsakaninsu.

A sakamakon haka, majalisar ta tura batun zuwa Kwamitinta na Ladabtarwa da Ɗa’a don gudanar da bincike.

A zaman kwamitin na ranar Laraba, Shugaban Kwamitin, Sanata Neda Imasuen (PDP, Edo ta Kudu), ya nuna takaicinsa kan rashin halartar Natasha.

Ya ce: “Sanata Natasha an gayyace ta zuwa wannan taro. Muna fatan za ta zo yayin da muke ci gaba da zama.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Malaman Musulmi ta yi kira da a dakatar da kisan kiyashi a Gaza cikin gaggawa

Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta fitar da wata sanarwa inda ta bayyana cewa laifuffukan gwamnatin sahyoniyawa a Gaza sun ketare dukkanin iyakokin kasa da kasa, tare da yin kira da a kawo karshen kashe-kashen mata da kananan yara da makamai masu guba, da yunwa, kishirwa, da cututtuka.

A cewar jaridar Arabi 21, kungiyar malaman musulmi ta duniya ta yi kira ga duniya da ta bayyana goyon bayanta ga al’ummar Palasdinu ta hanyar daukar matakan gaggawa da suka hada da dukkanin hanyoyin soja, tattalin arziki, da diflomasiyya mai  inganci.

Dangane da haka ne kungiyar ta yi kira ga limaman masallatan Juma’a a fadin duniya da su sadaukar da hudubar sallar Juma’a na gobe don magana kan wajabcin magance wahalhalu da radadin al’ummar Palastinu da kuma bukatar kawo karshen kisan gillar da gwamnatin sahyoniya ta ke yi wa Palastinawa.

Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta jaddada a cikin wannan bayani cewa, wannan cibiyar ta bibiyi matukar damuwa da bakin ciki da kisan gilla, da laifukan yaki , da yunwa da kishirwa, da kuma gudun hijira da gwamnatin yahudawan sahyoniya tare da goyon bayan ma’abota girman kan duniya suka saka mazauna Gaza a ciki.

Kungiyar ta kuma yi kira ga kasashen duniya da kungiyoyin kare hakkin bil adama da su ci gaba da tallafawa Gaza da kuma tattara laifukan da ake aikatawa har sai an dakatar da harin, da kuma tabbatar da adalci. Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta kuma yi kira da a gudanar da jerin gwano na lumana bayan sallar Juma’a a gobe a dukkanin kasashen musulmi, domin bayyana goyon bayansu ga zirin Gaza da kuma yin Allawadai da ayyukan wuce gona da irin Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Al-Houthi: Hare-haren Amurka sun kasa dakatar da gwagwarmayar Yeman
  • An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labarai
  • APC Ce Ke Min Bita-Da-Ƙulli Wajen Yi Min Kiranye – Sanata Natasha
  • Shugaban Kasar Iran Ya Fadawa Muhammad Bin Salman Kan Cewa Tehran Tana Shirin Kare Kanta
  • Trump na shan martani game da harajin da ya laftawa kasashen duniya
  • Kungiyar Malaman Musulmi ta yi kira da a dakatar da kisan kiyashi a Gaza cikin gaggawa
  • Ƙoƙarin Tsige Sanata Natasha Ya Gaza Cika Ƙa’idar Doka – INEC
  • INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye