Idan Kunne Ya Ji, Jiki Ya Tsira
Published: 6th, March 2025 GMT
Har ila yau, jim kadan bayan ficewar Zelenskyy daga Washington, shugabannin kasashen Turai da suka hada da na Jamus da Faransa da Italiya da kuma Birtaniya suka yi gaggawar mara masa baya, yayin da wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka suka yi kakkausar suka ga Ukraine wanda a cewar Sanata Lindsey Graham na jam’iyyar Republican ta South Carolina, “sanadiyyar wannan ganawar da ta bar baya da kura, ka iya kawo karshen goyon bayan Washington ga Kyiv.
Shin abin tambaya a nan, da gaske ne wannan yunkurin na Amurka don kawo karshen rikici ne a tsakanin Ukraine da Rasha ko kuwa don amfanin kanta ne? Me ya sanya gwamnatin Trump ta fara wani gangamin tonon silili mai zafi kan Zelenskyy?
Kwanakin baya sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya yi nuni da cewa, yunkurin Ukraine na shiga kungiyar NATO abu ne mara tabbas, tare da bai wa Kyiv shawarar daina fatan mallakar wani yankin kasa daga Rasha. Washington ta tattauna da Moscow a Saudi Arabia ba tare da Kyiev ba, wanda hakan ke nuna cewa za a iya yanke shawarar makomar Ukraine ba tare da saninta ba.
Bugu da kari, Trump ya kira Zelenskyy a matsayin “mai mulkin kama karya,” yana zargin Kyiv da fara tsokano rikici da Moscow. Sannan ya bukaci Zelenskyy ya rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adinai da Amurka da sauri, in ba haka ba, zai iya rasa duka kasarsa ga Rasha. A yayin ganawarsu ta ranar Juma’a, Trump ya zargi Zelenskyy da yunkurin kawo yakin duniya na uku. Duk wannan barazanar don cimma muradan son zuciyar Amurka na matsawa Kyiev rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adanai.
Wannan a fili yake, Amurka tana son dawo da kudadenta na tallafin soji da ta bai wa Ukraine na tsawon shekaru ba don neman zaman lafiyar yankin ba.
Don haka, Trump ya ki la’akari da bukatar Zelenskyy na neman tabbatar masa da tsaro sai dai matsa masa kan amincewa da yarjejeniyar hakar ma’adanan Ukraine.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Najeriya Ta Shirya Aiwatarda Yarjejeniyar Fahimta Tsakanin NTA, FRCN Da China Media Group
Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya jaddada kudurin Najeriya na aiwatar da cikakken yarjejeniyar biyu da aka kulla tsakanin China Media Group da manyan gidajen watsa labarai na gwamnati a Najeriya – Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) da Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN) a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a Beijing.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi Jakadan Sin a Najeriya, Mista Yu Dunhai, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa a yau alhamis. Ya ce, wadannan yarjejeniyoyi sun ƙudiri aniyar ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin watsa labarai da sadarwa, domin inganta dangantakar Najeriya da Sin.
Ya bayyana cewa yarjejeniyoyin sun shafi musayar bayanai da fasahar zamani, wanda hakan zai inganta ƙwarewar gidajen watsa labaran Najeriya tare da ɗaukaka su zuwa matakin da ya dace da kyawawan ƙa’idojin duniya.
“Najeriya da Sin a matakin hulɗar diflomasiyya suna da ƙawance mai ƙarfi matuka. Wannan ya haifar da sanya hannu kan yarjejeniyar fahimta guda 10 a Beijing, kuma guda biyu daga cikinsu suna da nasaba da wannan ma’aikata. Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) ita ce cibiyar talabijin mafi girma a duk faɗin Afirka, tana da tashoshi sama da 100 da ke rufe dukkan yankuna tare da isa ga mutane sama da miliyan 200. Yana da matuƙar muhimmanci, kuma abin da NTA ke son cimmawa ta hanyar wannan haɗin gwiwa da Sin shi ne musayar labarai, fasaha, da bayanai wanda zai amfanar da ƙasashen biyu. Haka kuma, muna da irin wannan yarjejeniya da ɗaya daga cikin manyan gidajen rediyo a Afirka, wato Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN). Wadannan yarjejeniyoyi sun riga sun kammala, kuma Najeriya tana da niyyar cika nata ɓangaren,” in ji shi.
Ministan ya ce, bayar da sahihin bayani da labarai na gaskiya zai ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashe, don haka ya nemi haɗin gwiwa da Sin wajen yaƙi da labaran ƙarya, ɓata bayani da yada bayanai na bogi.
“Yada labaran ƙarya ƙalubale ne ga duniya baki ɗaya. Mun san cewa Sin tana ɗaukar wannan batu da muhimmanci sosai, haka kuma mu ma a Najeriya muna ɗaukar hakan da muhimmanci. Ba matsala ba ce da ke shafar Najeriya da Sin kaɗai; matsala ce ta duniya baki ɗaya, kuma muna son yin aiki tare da Sin don yaƙi da labaran ƙarya tare da inganta watsa labarai masu amfani da za su taimaka wajen bunƙasa al’umma,” in ji shi.
Idris ya bayyana wa Jakadan cewa, Najeriya na da ‘yancin watsa labarai a matsayin wani muhimmin bangare na manufofin gwamnatin Tinubu don ƙarfafa dimokuradiyya ta hanyar bayar da ingantattun bayanai.
“Kafafen watsa labarai a nan suna da ’yanci sosai. Tabbas, akwai wasu matsaloli a lokaci zuwa lokaci, wanda koyaushe muna aiki a kansu don ingantawa. Najeriya na da babbar ’yancin watsa labarai, kuma muna so mu ci gaba da hakan,” in ji shi.
Ministan ya kuma bukaci kamfanonin Sin su yi amfani da sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa domin zuba jari a tattalin arzikin Najeriya.
A nasa jawabin, Jakada Dunhai ya ce a matsayinsa na sabon jakadan Sin a Najeriya, zai yi duk mai yiwuwa don ƙara ƙarfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.
Ya nuna goyon bayansa ga shirin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Tinubu, wanda ke da nufin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa don samar da ci gaba mai dorewa.
“A matsayina na sabon jakada, ina ganin kaina a matsayin mai sa’a saboda na zo ne a lokacin da Najeriya ke karkashin jagorancin Shugaba Tinubu, wanda ke da niyyar gina ƙasa mai ƙarfi. Haka nan, a karkashin jagorancin Shugaba Xi Jinping, Sin tana kan tafarkin sabunta ƙasa ta hanyar tsarin zamani na Sin,” in ji shi.
Jakadan ya tunatar da cewa a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a Beijing, Shugabannin kasashen biyu, Xi Jinping da Tinubu, sun amince da ɗaukaka dangantakar kasashen su zuwa babbar kawance ta fuskar diflomasiyya, wanda hakan zai buɗe sabon babi a dangantakar su.
Ya ce yana sa ran ganin yadda za a aiwatar da yarjejeniyoyin fahimta da aka kulla tsakanin NTA, FRCN da China Media Group, domin kafafen yada labarai suna da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen gina al’umma.
Jakadan ya bayyana jin daɗinsa cewa kafafen watsa labarai a Najeriya suna daidaito, gaskiya da adalci a labaran da suke watsawa, domin suna ƙoƙarin gabatar da cikakken bayani kan abubuwan da ke faruwa ga ‘yan Najeriya.
A bangaren zuba jari, Jakadan ya ce Shugaba Xi Jinping ya alkawarta dala biliyan 50 domin zuba jari a Afirka a cikin shekaru uku masu zuwa, a matsayin ci gaba ga yarjejeniyoyin fahimta guda goma da aka rattaba hannu a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a baya-bayan nan.
Cov/Adamu Yusuf