HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Sheikh Hassan Jingir a Jos
Published: 6th, March 2025 GMT
Dubban al’ummar Musulmi ne suka halarci jana’izar Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Izala na Ƙasa, Sheikh Hassan Jingir, a garin Jos.
An gudanar da sallar jana’izar ne a ranar Alhamis a unguwar Anguwan Rimi da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na watanni 6 An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a BinuwaiA cewar sakataren yaɗa labaran JIBWIS, Ahmad Ashiru, Sheikh Jingir ya rasu yana da shekara 70.
Ya rasu a gidansa da ke Jos bayan fama da rashin lafiya.
Ya rasu ya bar mata biyu da yara sama da 40.
Ga hotunan yadda aka yi jana’izar:
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Benuwe, ta ceto fasinjoji 14 da wasu ’yan bindiga suka sace yayin da suke tafiya a kan hanyar Makurdi zuwa Otukpo.
Sai dai uku daga cikin fasinjojin sun rasu, ciki har da direban motar.
Sabon harajin Trump zai jefa tattalin arziƙin duniya cikin matsala — WTO Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin KanoA cewar sanarwar da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Catherine Anene, ta fitar a ranar Juma’a, lamarin ya faru ne a ranar 3 ga watan Afrilu, 2025.
Wasu ’yan bindiga sun farmaki motar a yankin Otukpo Burnt Bricks, inda suka buɗe wa direban da wani fasinja da ke gaba wuta, lamarin da ya tilasta direban tsayawa.
’Yan sanda tare da jami’an tsaro sun isa wajen da abin ya faru cikin gaggawa.
Sun iske direban da wani fasinja a cikin mota kwance cikin jini, amma an garzaya da su asibiti, inda aka tabbatar da mutuwarsu.
’Yan bindigar sun yi awon gaba da sauran fasinjojin zuwa cikin daji.
A ranar 4 ga watan Afrilu, ’yan sanda sun bi sahunsu zuwa cikin dajin inda suka yi musayar wuta, wanda hakan ya sa suke tsere suka bar mutanen da suka sace.
Biyu daga cikin waɗanda aka sace an yi musu rauni da adda kafin a ceto su.
An samu nasarar ceto mutum 14, amma ɗaya daga cikinsu ya rasu a asibiti, sauran kuma suna karɓar magani.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Steve Yabanet, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, kuma ya sha alwashin kamo maharan.
Ya kuma buƙaci al’ummar Otukpo da su kai rahoton duk wanda suka gani da raunin harbin bindiga, domin an jikkata wasu daga cikin ’yan bindigar yayin artabu da jami’an tsaro.