HausaTv:
2025-03-06@19:03:07 GMT

Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta yi kira da a tallafa wa Falasdinawa

Published: 6th, March 2025 GMT

Sakatare-janar na kungiyar malaman musulmi ta duniya ya yi kira ga shugabannin kasashen Larabawa da su hada kai da al’ummarsu wajen goyon bayan Falasdinawa.

Babban sakataren kungiyar malaman musulmi ta duniya Ali Muhammad Al-Salabi, ya yi kakkausar suka kan ci gaba da goyon bayan da Amurka ke yi wa haramtacciyar kasar Isra’ila, yana mai bayyana hakan a matsayin taka rawa a cikin laifukan da take aikatawa kan al’ummar Palastinu.

Ya yi nuni da cewa, wannan tallafin na nuni da nuna son kai na siyasa da ke neman boye laifukan kisan kare dangi take aikatawa kan fararen hular zirin Gaza da ba su da kariya.

A cikin jawabinsa, Al-Salabi ya yi kira ga gwamnatocin kasashen Larabawa da na Musulunci da su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi, tare da ba da goyon baya ga al’ummar Palastinu.

Babban sakataren kungiyar kasashen musulmi ta duniya ya jaddada cewa, alhakin ceto al’ummar Palastinu, bisa la’akari da goyon bayan da manyan kasashen duniya suke bayarwa ga gwamnatin sahyoniyawan ya rataya a wuyan gwamnatocin musulmi, da  kasashen Larabawa da kuma ‘yantattun al’ummomi  naduniya.

Haka nan kuma ya yi kira ga muhimman cibiyoyin Musulunci karkashin jagorancin Al-Azhar da su yi amfani da dukkan hanyoyin da ake da su na matsin lamba wajen ceto Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: musulmi ta duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Kasashen Turai Don Goyon Baya Ga Kasar Ukraine, Ya Watse Ba Tare Da Tsaida Irin Taimakon Da Zasu Yi Mata Ba

Shuwagabannin kasashen Turai da wakilai daga kasashe 19 na Kungiyar, sun kammala taro a birnin Lodon, inda suka nuna goyon bayansu ga kasar Ukraine, musamman kan yadda ya dage wajen kare kasarsa da kasashen Turai  a gaban Donal Trum a ranar Jumma’an da ta gabata, ya waste ba tare da kasashen sun bayyana abinda zasu iya yiwa Ita Ukraine a yakin da take ci gaba da fafatawa da Rasha ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa matsalolin da suka taso dangane da dogaron da kasashen turai suke yi kan kungiyar Tsaro ta NATO yana daga cikin manya-manyan al-amura da suka tattauna.

Yakin cacarbakin da shugaba Trump na Amurka yayi da shugaban kasar Ukraine ya zama masomin kawo sauye-sauye masu yawa a dangantakar kasashen da Amurka.

Firai ministan kasar Ukraine Keir Starmer ya gabatar da shawara mai matakai 4 ta taimakawa kasar ta Ukraine a yakin da taek fafatawa da kasar Rasha. Sannan shuwagabannin kasashen turai sun bukaci a samar da wata cibiyar tsaron kasashensu ba tare da dogaro da kasar Amurka ba.

Har’ila yau shugaban kungiyar tarayyar ta Turai Ursula Von der Leyen ya bukaci a gaggauta samar da hanyar tsaron kasashen na turai da gaggawa.

   

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Kira Ga Al’ummar Musulmi Da Su Kara Yawan ‘Ya’yan Itatuwa Da Sha A Ramadan
  • Majiyar Fadar Shugaban Kasar Amurka Tace Ta Shiga Tattaunawa Kai Tsaye Da Kungiyar Hamas A Gaza
  • Trump Ya Yi Barazanar Korar Daliban Da Ke Goyon Bayan Falasdinawa
  • Hamas Ta Yi Maraba Da Shirin Sake Gina Gaza Da Taron Kasashen Larabawa Ya Gabatar
  • Kungiyar Hamas Ta Ki Amincewa Da Kwance Damarar Kungiyar A Gaza
  • Taron Kasashen Turai Don Goyon Baya Ga Kasar Ukraine, Ya Watse Ba Tare Da Tsaida Irin Taimakon Da Zasu Yi Mata Ba
  • MDD Ta Nuna Cikakken Goyon Bayanta Ga Shirin Sake Gina Gaza Da Larabawa Su Ka Gabatar
  • Hamas Ta Ce Yarjeniyar Tsagaita Wuta Ne Kadai Za Ta Kubutar Da Fursinonin Yahudawa Daga Hannun Kungiyar
  • Angola Zata Shiga Shirin ‘Yankunan Kasuwanci’ Na Kungiyar SADC