Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman
Published: 6th, March 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya dage dakatarwar da aka yi wa mai bashi shawara na musamman kan harkokin albashi da fansho, Bashir Ado Kazaure da aka mishi a baya ba tare da bata lokaci ba.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Jigawa Malam Bala Ibrahim ya sanyawa hannu kuma ya bai wa manema labarai.
Sanarwar ta bayyana cewa, matakin na zuwa ne bayan wani kwakkwaran bincike da kwamitin da aka kafa karkashin jagorancin babban lauyan gwamnati kuma kwamishinan shari’a na jihar Barista Bello Abdulkadir Fanini ya gudanar.
“Rahoton kwamitin ya yi tsokaci kan al’amuran da suka dabaibaye dakatarwar da aka yi wa Bashir Kazaure, biyo bayan sanarwar batun biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 kafin lokacin da gwamnati ta shirya sanarwa a hukumance,” in ji shi.
Sakataren gwamnatin jihar ya bayyana cewa, matakin dage dakatarwar na nuni da yadda Gwamnan ya jajirce wajen tabbatar da adalci da bin doka da oda wajen tafiyar da al’amura.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta Bayyana cewa: TattaunawarMuscat Wata Dama Ce Ta Samun Zaman Lafiya Kan Batutuwan Masu Sarkakiya
Mai ba da shawara ga Jagoran juya juya halin Musulunci kan harkokin siyasa ya bayyana cewa: Tattaunawar Muscat wata dama ce ta samun zaman lafiya kan batutuwa masu sarkakiya
Ali Shamkhani mai ba Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara kan harkokin siyasa ya yi tsokaci kan tattaunawar ba na kai tsaye ba da ake yi tsakanin Iran da Amurka a babban birnin kasar Omani na Muscat.
A cikin jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na twitter, Shamkhani ya bayyana cewa: Fiye da kwanaki 100 ke nan da Trump ya hau kan karagar mulki, yana mai cewa: “Ba a warware manyan batutuwan da suka shafi Yemen, Gaza, Ukraine, da rikicin haraji ba, baya ga gibin kasafin kudi, har yanzu ba a warware ba.”
Ya ci gaba da cewa: “A cikin wannan yanayi, tattaunawar Muscat ta bayyana a matsayin wata dama ta samun nasara ta hadin gwiwa tsakanin bangarorin da abin ya shafa (Amurka da Iran).”
Shamkhani ya kammala rubutunsa a twitter da cewa: Wadannan shawarwarin sun ginu ne a kan manyan ka’idoji guda uku: gaskiya (wanda ke tabbatar da cewa babu wata karkata daga manufofin da aka sa gaba); Ma’auni (wanda ke buƙatar ɗaga duk takunkumin da aka sanya); Da kuma bin doka (wanda ke ba da tabbacin haƙƙin haɓakawa cikin tsarin dokokin ƙasa da ƙasa).