HausaTv:
2025-03-06@19:02:03 GMT

ECOWAS Za Ta Aika Kwamitin Sulhu Zuwa Kasashen AES

Published: 6th, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin ECOWAS, ta kafa wani kwamiti na musamman domin tattaunawa da shugabannin kasashen Burkina Faso, Mali, da Nijar da suka fice daga kungiyar, tare da kokarin magance matsalolin siyasa a yankin Yammacin Afirka.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Barau Jibrin, wanda mamba ne a Majalisar ECOWAS, ya tabbatar da haka a wata tattaunawa da ya yi da manema labarai.

Ya ce an yanke wannan shawara ne bayan wani taro da aka gudanar a Legas.

A cewar Sanata Barau, manufar kwamitin ita ce tattaunawa da shugabannin kasashen AES don fahimtar juna da jaddada muhimmancin ci gaba da kasancewa cikin ECOWAS, musamman idan aka yi la’akari da dangantakar tattalin arziki da zamantakewa da ke tsakanin jama’ar yankin.

Shugabar Majalisar Dokokin ECOWAS, Hadja Memounatou Ibrahima, ta ce kafa kwamitin zai taimaka wajen shawo kan matsalolin siyasa a yankin da kuma hana ƙarin ƙasashen Yammacin Afirka ficewa daga ECOWAS.

A ranar 29 ga watan Janairu, 2025, kasashen Burkina Faso, Mali, da Nijar – waɗanda suka hade a karkashin Kawancen Kasashen Sahel (AES) – sun sanar da ficewarsu daga ECOWAS.

Duk da hakan, ECOWAS ta tabbatar da cewa babu wata matsala a ɓangaren sufuri da kasuwanci tsakanin kungiyar da kasashen AES, domin har yanzu ana ci gaba da hulda tsakanin al’ummomin yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Kasashen Turai Don Goyon Baya Ga Kasar Ukraine, Ya Watse Ba Tare Da Tsaida Irin Taimakon Da Zasu Yi Mata Ba

Shuwagabannin kasashen Turai da wakilai daga kasashe 19 na Kungiyar, sun kammala taro a birnin Lodon, inda suka nuna goyon bayansu ga kasar Ukraine, musamman kan yadda ya dage wajen kare kasarsa da kasashen Turai  a gaban Donal Trum a ranar Jumma’an da ta gabata, ya waste ba tare da kasashen sun bayyana abinda zasu iya yiwa Ita Ukraine a yakin da take ci gaba da fafatawa da Rasha ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa matsalolin da suka taso dangane da dogaron da kasashen turai suke yi kan kungiyar Tsaro ta NATO yana daga cikin manya-manyan al-amura da suka tattauna.

Yakin cacarbakin da shugaba Trump na Amurka yayi da shugaban kasar Ukraine ya zama masomin kawo sauye-sauye masu yawa a dangantakar kasashen da Amurka.

Firai ministan kasar Ukraine Keir Starmer ya gabatar da shawara mai matakai 4 ta taimakawa kasar ta Ukraine a yakin da taek fafatawa da kasar Rasha. Sannan shuwagabannin kasashen turai sun bukaci a samar da wata cibiyar tsaron kasashensu ba tare da dogaro da kasar Amurka ba.

Har’ila yau shugaban kungiyar tarayyar ta Turai Ursula Von der Leyen ya bukaci a gaggauta samar da hanyar tsaron kasashen na turai da gaggawa.

   

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Jinping Ya Ziyarci Mambobin Majalisar CPPCC
  • ECOWAS Za Ta Aika Kwamitin Sulhu Zuwa Ƙasashen AES
  • Jakadan Iran A Hukumar IAEA Ya Ce Takunkuman Kasashen Yamma A Kan Kasar Ba Za Su Yi Aiki Ba
  • Mutanen Afrika Sun Kori Kasar Faransa Daga Kashensu Ne Saboda Ta Ki Ta Amince Da Yencinsu
  • Taron Kasashen Turai Don Goyon Baya Ga Kasar Ukraine, Ya Watse Ba Tare Da Tsaida Irin Taimakon Da Zasu Yi Mata Ba
  • Yemen Ta Gargadi HKI Kan Ci Gaba Da Hana Shigar Kayakin Agaji Zuwa Yankin Gaza
  • Masar: An Kawo Karshen Taron Kasashen Larabawa Na Musamman Akan Gaza
  • Kremlin: Putin Ya Amince Da Shiga Tsakanin Iran Da Amurka
  • Masu Alaka