Aminiya:
2025-04-27@22:51:12 GMT

Hukumar Zaɓen Neja ta sanar da ranar zaɓen ƙananan hukumomoni

Published: 6th, March 2025 GMT

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Jihar Neja ta sanya ranar 1 ga watan Nuwamba, 2025 domin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi.

Shugaban Hukumar Zaɓen, Mohammed Jibrin Iman ne ya bayyana haka a lokacin da yake ƙaddamar da jadawalin ayyukan gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi na shekarar 2025 a hedikwatar hukumar da ke Minna, babban birnin jihar.

Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na watanni 6 Gwamnatin Ogun ta rufe kamfanoni saboda mutuwar ma’aikata

Imam ya ce an fara shirye-shiryen zaɓen ne daga ranar 6 ga watan Maris, 2025, yana mai cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyu ne tsakanin ranakun 15 zuwa 24 ga Maris, 2025, yayin da za a tattara fom da kuma jerin sunayen ’yan takara za su gudana daga ranar 25 ga Maris zuwa 2 ga Afrilu, 2025.

Shugaban ya ce, za a maido da jerin sunayen ’yan takarar da aka tura musu daga ranar 3 zuwa 10 ga Afrilu yayin da za a wallafa bayanan ’yan takarar daga ranar 11 zuwa 18 ga Afrilu, 2025.

Ya ƙara da cewa an shirya tattara fom ɗin tsayawa takara a ranar 19 zuwa 26 ga Afrilu yayin da jam’iyyun siyasa za su gabatar da fom ɗin takara daga ranar 27 ga Afrilu zuwa 3 ga Mayu, 2025.

Ya ce, za a fara gangamin yaƙin neman zaɓen daga ranar 27 ga watan Mayu har zuwa ranar 31 ga Oktoba, 2025.

Imam ya tabbatar wa jam’iyyun siyasa matakin da za a yi na gudanar da zaɓuka cikin ’yanci, gaskiya da adalci bisa wasu dokoki da jagororin gudanar da zaɓukan kansiloli.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe sojoji 12 a barikin Nijar

An kashe sojoji 12 a yankin Tillaberi na yammacin ƙasar mai iyaka da Mali da Burkina Faso, yankin da ke zama tungar masu iƙirarin jihadi da ’yan ina da kisa masu nasaba da ’yan ƙungiyoyin al Qaeda da IS.

Ma’aikatar tsaron Nijar ta sanar da cewa an yi wa dakarunta na bataliyar ko-ta-kwana mai suna Almahao kwanton ɓauna ne a wani kauye da ke kusa da Sakoira na yammacin Tillaberi, inda sojan suka jima suna ɓarin wuta da ’yan ta’adda kafin a kawo musu ɗauki.

An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa

Gwamnatin ta bayyana cewa tuni ta cafke mutane biyu da ake zargi da kai harin a barikin sojojin da ke da nisan mil shida daga ƙauyen Sakoira a jihar ta Tillaberi.

A baya gwamnatin ƙasar ta sanar da kashe ’yan ta’adda tara, ta kuma ƙwace makamai daga hannu masu iƙirarin jihadi da suka kai wani harin da ta daƙile a yankin.

A yankin Tahoua mai iyaka da Nijeriya, rundunar tsaron Nijar ɗin ta sanar da ɗauki ba dadi da Lakurawa masu yawan yin kutse kuma suna kai hari ga bututun man fetur ɗinta da ke zuwa gaɓar teku a Benin.

Nijar Mali da kuma Burkina faso sun shafe sama da shekaru 10 ƙarƙashin barazanar ƴan ta‘adda masu iƙirarin jihadi da ke afkawa jami’an tsaro da kuma fararen hula lokaci zuwa lokaci.

To sai dai kuma ƙididdiga ta nuna ƙaruwar kai hare-hare tun bayan da sojojin ƙasashen uku suka yanke shawarar kifar da gwamnatin fararen hula.

Rikicin yankin Sahel da ya samo asali daga ƙasar Mali a 2012, wanda kuma ya faɗaɗa har zuwa ƙasashen Burkina Faso da Nijar da kuma Benin da ya halaka dubban mutane kama daga sojoji har zuwa farar hula.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  • Falasdinawa 39 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’o’I 24
  •  Adadin Wadanda Su ka Kwanta Dama A Gobarar Tashar Jirgin Ruwan Shahid Raja’i Sun Kai 21
  • Hukumar Alhazan Jihar Kaduna Ta Wajibta Gudanarda Binciken Lafiya Ga Maniyatan 2025
  • Yadda Za A Gudanar Da Zaben Sabon Paparoma Da Zai Gaji ‘Pope Francis’
  • Magidanci ya kashe kansa saboda mutuwar matarsa a Neja 
  • ‘Yan Bindiga Na Kakaba Harajin Miliyoyin Naira Ga Mutanen Zamfara
  • Hajji 2025: Hukumar Alhazan Yobe ta gudanar da taro don mahajjata
  • Kudaden Da Ke Hannun Mutane Sun Ragu Zuwa Naira Tiriliyan 5 – Rahoto
  • Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP