Hukumar Zaɓen Neja ta sanar da ranar zaɓen ƙananan hukumomoni
Published: 6th, March 2025 GMT
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Jihar Neja ta sanya ranar 1 ga watan Nuwamba, 2025 domin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi.
Shugaban Hukumar Zaɓen, Mohammed Jibrin Iman ne ya bayyana haka a lokacin da yake ƙaddamar da jadawalin ayyukan gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi na shekarar 2025 a hedikwatar hukumar da ke Minna, babban birnin jihar.
Imam ya ce an fara shirye-shiryen zaɓen ne daga ranar 6 ga watan Maris, 2025, yana mai cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyu ne tsakanin ranakun 15 zuwa 24 ga Maris, 2025, yayin da za a tattara fom da kuma jerin sunayen ’yan takara za su gudana daga ranar 25 ga Maris zuwa 2 ga Afrilu, 2025.
Shugaban ya ce, za a maido da jerin sunayen ’yan takarar da aka tura musu daga ranar 3 zuwa 10 ga Afrilu yayin da za a wallafa bayanan ’yan takarar daga ranar 11 zuwa 18 ga Afrilu, 2025.
Ya ƙara da cewa an shirya tattara fom ɗin tsayawa takara a ranar 19 zuwa 26 ga Afrilu yayin da jam’iyyun siyasa za su gabatar da fom ɗin takara daga ranar 27 ga Afrilu zuwa 3 ga Mayu, 2025.
Ya ce, za a fara gangamin yaƙin neman zaɓen daga ranar 27 ga watan Mayu har zuwa ranar 31 ga Oktoba, 2025.
Imam ya tabbatar wa jam’iyyun siyasa matakin da za a yi na gudanar da zaɓuka cikin ’yanci, gaskiya da adalci bisa wasu dokoki da jagororin gudanar da zaɓukan kansiloli.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Benuwe, ta ceto fasinjoji 14 da wasu ’yan bindiga suka sace yayin da suke tafiya a kan hanyar Makurdi zuwa Otukpo.
Sai dai uku daga cikin fasinjojin sun rasu, ciki har da direban motar.
Sabon harajin Trump zai jefa tattalin arziƙin duniya cikin matsala — WTO Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin KanoA cewar sanarwar da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Catherine Anene, ta fitar a ranar Juma’a, lamarin ya faru ne a ranar 3 ga watan Afrilu, 2025.
Wasu ’yan bindiga sun farmaki motar a yankin Otukpo Burnt Bricks, inda suka buɗe wa direban da wani fasinja da ke gaba wuta, lamarin da ya tilasta direban tsayawa.
’Yan sanda tare da jami’an tsaro sun isa wajen da abin ya faru cikin gaggawa.
Sun iske direban da wani fasinja a cikin mota kwance cikin jini, amma an garzaya da su asibiti, inda aka tabbatar da mutuwarsu.
’Yan bindigar sun yi awon gaba da sauran fasinjojin zuwa cikin daji.
A ranar 4 ga watan Afrilu, ’yan sanda sun bi sahunsu zuwa cikin dajin inda suka yi musayar wuta, wanda hakan ya sa suke tsere suka bar mutanen da suka sace.
Biyu daga cikin waɗanda aka sace an yi musu rauni da adda kafin a ceto su.
An samu nasarar ceto mutum 14, amma ɗaya daga cikinsu ya rasu a asibiti, sauran kuma suna karɓar magani.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Steve Yabanet, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, kuma ya sha alwashin kamo maharan.
Ya kuma buƙaci al’ummar Otukpo da su kai rahoton duk wanda suka gani da raunin harbin bindiga, domin an jikkata wasu daga cikin ’yan bindigar yayin artabu da jami’an tsaro.