Aminiya:
2025-03-06@20:08:53 GMT

An kama ’yan Pakistan biyu da laifin yin garkuwa a Legas

Published: 6th, March 2025 GMT

Jami’an hukumar ’yan sandan Jihar Legas sun kama wasu ’yan ƙasar Pakistan guda biyu, Roman Gull mai shekara 19 da kuma Aftab Ahmad mai shekara 28 bisa zargin jagorantar wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a jihar.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa waɗanda ake zargin tare da wasu mutum biyar ne, sun kama wani ɗan ƙasar Pakistan mai shekara 48 ɗan asalin Jihar Kano da tayin aikin bogi a matsayin mai dafa abinci kafin su yi awon gaba da shi tare da neman kuɗin fansa miliyan 50 daga ma’aikacin nasa.

Hukumar Zaɓen Neja ta sanar da ranar zaɓen ƙananan hukumomoni Sheikh Sa’idu Hassan Jingir ya rasu

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, inda ya ce jami’an sashin Ikeja sun kai ɗaukin gaggawa inda suka yi nasarar ceto wanda abin ya shafa.

Sai dai wasu ’yan ƙungiyar sun yi nasarar tserewa.

“An samu kiran gaggawa a cibiyar ofishin Ikeja na rundunar ’yan sandan Jihar Legas a ranar Laraba, 5 ga Maris, 2025, game da sace wani ɗan Pakistan mai shekara 48 a Ikeja.

Hundeyin ya ce, “An tura tawagar da ke yaƙi da masu aikata laifuka cikin gaggawa, lamarin da ya kai ga ceto wanda aka kashe tare da kama biyu daga cikin waɗanda suka yi garkuwa da shi, Roman Gull da Aftab Ahmad, ‘yan ƙasar Pakistan, yayin da wasu biyar suka tsere.”

Binciken farko ya nuna cewa waɗanda aka kama tare da abokan aikinsu sun yaudari wanda aka azabtar zuwa Legas ta hanyar yi masa alƙawarin aiki a matsayin ma’aikaci mai dafa abinci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane mai shekara

এছাড়াও পড়ুন:

An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Binuwai

Daliban da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Jami’ar Tarayya ta Joseph Sarwuan Tarka da ke Jihar Binuwai sun kubuta.

Daliban sun lubauta ne bayan shafe kwanaki takwas a hannun ’yan ta’addan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban NAN:Muna Iya Ganin Basirar Sin Ta Manyan Taruka Biyu Da Take Gudanarwa Yanzu
  • An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Binuwai
  • An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna
  • Mutum 2 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Gini Ya Rufta A Legas
  • An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai
  • Mutum 2 sun rasu, 6 sun jikkata yayin da gini ya rufta a Legas
  • An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Dokokin Kasar Sin
  • Majalisar Bayar Da Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ta Fara Taronta Na Shekara-shekara
  • Bidiyon batsa: Kotu ta ɗaure ’yan Tiktok biyu a Kano