Yayin da tattalin arzikin kasar Sin ke kara samun tagomashi, masana daga sassa daban daban, na ganin hakan dama ce ta ci gaban duniya baki daya. Kamar dai yadda sakamakon wani bincike, na asusun ba da lamuni na duniya IMF ya nuna yadda bunkasar tattalin arzikin kasar Sin ke shafar ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

Binciken ya nuna bunkasar tattalin arzikin Sin da karin kaso daya bisa dari, yake haifar da matsakaicin bunkasar tattalin arzikin sauran sassan kasa da kasa da kaso 0.3 bisa dari.

Duba da haka, ma iya cewa duniya za ta ci gaba da shan romon bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, yayin da kasar ke ta kara fadada manufofinta na bude kofa ga sassan duniya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: bunkasar tattalin arzikin

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Dole Ne Amurka Ta Janye Mata Takunkuman Tattalin Arziki Masu Gurgurtawa Da Ta Dora Mata

Mataimakin ministan harkokin wajen a kan al-amuran siyasa, dole ne Amurka ta daukewa kasarsa wadannan takunkuman tattalin arziki wanda suke cutar da mutanen kasar Iran da al-adunsa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto TakhtaRawanchi yana fadar haka a shafinsa na X ko twitter a da, a kuma  jiya Talata, Mataimakin ministan ya kara da cewa, takunkuman tattalin arzikin da kasashen Amurka da Turai suka dorawa kasar Iran ya zuwa yanzu ya shafi rayuwar mutanen kasar da dama wanda kuma take hakkinsu ne.

Labarin ya kara da cewa a shekaru fiye da 40 da suka gabata, gwamnatocin Amurka kadai sundorawa kasar Iran takunkuman tattalin arziki mafi muni, kuma nau’ii daban-daban. Haka ma ta dade tana wa kasar barazanar far mata da yaki, takunkuman tattalin arziki mafi muna, yakin farfaganda na kasya da sauransu.

Duk da cewa gwamnatocin kasar ta Amurka sun kasa cimma manufofinsu na dorawa kasar ta Iran takunkuman tattalin arziki,  Washington ta ci gaba da dorawa kasar wadannan takunkuman tattalin arziki. Duk da cewa hakan ya sabawa dokokin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Burin Gwamnatin Sin Na Bunkasa Gdp Da Kashi 5% A Bana Ya Bayyana Niyyarta Ta Samun Ingantaccen Ci Gaban Tattalin Arziki
  • Kasar Sin A Matsayin Katafariyar Cibiyar Kere-Keren Mutum-Mutumi A Duniya
  • Iran Ta Ce Dole Ne Amurka Ta Janye Mata Takunkuman Tattalin Arziki Masu Gurgurtawa Da Ta Dora Mata
  • Sin Na Matukar Adawa Da Manufar Kariyar Ciniki Da Babakeren Amurka
  • An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Dokokin Kasar Sin
  • Har Kullum Jama’ar Kasar Sin Suna Adawa Da Nuna Fin Karfi
  • Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Batutuwan Da Suka Shafi Sinadarin Fentanyl
  • Mai Magana Da Yawun NPC: Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Juriya Da Ginshiki Mai Kwari
  • Kakaki: A Ko Da Yaushe Kasar Sin Tana Tsayawa Tare Da Kasashe Masu Tasowa