Leadership News Hausa:
2025-03-06@22:19:40 GMT

Yadda Ake Ayyukan Gina Ababen More Rayuwa A Jihar Zamfara 

Published: 6th, March 2025 GMT

Yadda Ake Ayyukan Gina Ababen More Rayuwa A Jihar Zamfara 

Sanarwar ta ƙara da cewa, ziyarar wani bangare ne na tsarin Gwamna Dauda Lawal na tabbatar da ingantattun ayyuka a faɗin jihar da kuma tabbatar da kammala ayyukan a kan lokaci.

 

“A ranar Talata ne Gwamna Dauda Lawal ya fara ziyarar aiki domin duba ɗimbin ayyukan da gwamnatinsa ta fara aiwatarwa.

 

“An fara ziyarar ne da Babban Asibitin Gusau, ɗaya daga cikin manyan asibitocin da aka gyara, tare da samar mata da kayan aiki a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

A lokacin da yake duba aikin filin jirgin sama na Zamfara, Gwamna Lawal ya ce, gwamnatinsa ba wai kawai tana gina kowane irin filin jirgin saman ba ne, amma ana ginin ne na zamani wanda zai yi fice bisa ga dukkan alamu.

 

“Gwamnan ya nuna jin daɗinsa da yadda aikin ke gudana, wanda ya haɗa da titin jirgi da tasha.

 

“Gwamna Lawal ya kuma duba hanyar garin Rawayya da ke gudana da kuma aikin gina tsohuwar Titin Kasuwa zuwa mahaɗar Chemist na Nasiha.

 

“Sauran ayyukan da Gwamna Dauda Lawal ya duba a halin yanzu sun haɗa da gyaran kashi na biyu na Sakatariyar JB Yakubu ta Jihar, Kwalejin Kimiyya ta Zamfara (ZACAS), da kuma Makarantar Sakandaren Kimiyya ta Gwamnati.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

A yi adalci a binciken mutuwar dan kwallon Nijerirya a Uganda —Gwamnatin Sakkwato

Gwamnatin Sakkwato ta buƙaci a yi adalci a binciken da ake yi kan silar rasuwar ɗan ƙwallon ƙafan nan ɗan asalin jihar, Abubakar Lawal, wanda ya rasu a satin da ya gabata kasar Uganda inda yake taka leda.

Kwamishinan Matasa da Wasanni na jihar, Injiniya Almustafa Muhammad Kofar Marke ne ya sanar da hakan a lokacin da suke karbar gawar margayin a Nijeriya domin jana’izarsa a mahaifarsa sa ke jihar.

Injiniya Kofar Marke ya bayyana baƙin ciki da rashin Abubakar Lawal, wanda ya bayyana a matsayin ɗan kwallon ƙafa na musamman kuma jakada nagari a harkar wasanni.

“Labarin rasuwar nan abar girgiza da taba zuciya ce, domin marigayin ya bayar da gudunmuwa a harkaar ƙwallon ƙafa ta a-zo-a-gani a duniya ta hanyar ƙasashe daban-daban.

“Muna gode wa ofishin jekadancinmu da ya tabbatar da dawowar gawar margayin zuwa gida don yi mata janaza, haka ma makusantan abokansa suma sun yi kokari.”

Injiniya Mustafa ya ƙara tabbatar da goyon bayansu ga iyalan marigayin kamar yadda suka yi tsaye tun sa’adda lamarin ya faru har aka karbi gawar, bisa ga sahalewar gwamnan Sakkwato Ahmad Aliyu.

Dan kwallon Nijeriya Abdullahi Shehu ne ya rako gawar zuwa Nijeriya ya mika ta’aziyarsa ga iyalai da dangin margayin da mutanen Sakkwato da masoya kwallon kafa gaba daya.

“Abubakar Lawal ba kawai abokin hulɗa ba ne, aboki ne a gare ni, yana da karimci da sanin yakamata, ina rokon Allah Ya gafarta masa”.

Margayin ɗan kwallon Nijeriya ne da ya fara buga wasa a Sakkwato da Nasarawa kafin likafa ta ci gaba ya koma kasar Uganda, ya samu nasarori da dama a wasan ƙwallon kafa a lokacin rayuwarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Gwamnatinsa Na Bai Wa Sojoji Haɗin Kai 
  • Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman
  • A yi adalci a binciken mutuwar dan kwallon Nijerirya a Uganda —Gwamnatin Sakkwato
  • Gwamna Zamfara Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikata.
  • Gwamna Lawal Ya Yaba Da Yadda Aikin Filin Jirgin Saman Zamfara Ke Tafiya
  • Hamas Ta Yi Maraba Da Shirin Sake Gina Gaza Da Taron Kasashen Larabawa Ya Gabatar
  • NOA Ta Kara Daura Damarar Inganta Ayyukanta A Jihar Jigawa
  • Masar: An Kawo Karshen Taron Kasashen Larabawa Na Musamman Akan Gaza
  • MDD Ta Nuna Cikakken Goyon Bayanta Ga Shirin Sake Gina Gaza Da Larabawa Su Ka Gabatar