Aminiya:
2025-03-07@00:34:04 GMT

Ƙin yin sulhu da ’yan bindiga na haifar da alheri – Gwamnan Zamfara

Published: 6th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce matsayarsa na ƙin amincewa a yi sulhu da ’yan bindiga na taimakawa wajen dawo da zaman lafiya a jihar.

Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin da yake karɓi baƙuncin Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hassan Bala Abubakar.

An kama ’yan Pakistan biyu da laifin yin garkuwa a Legas HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Sheikh Hassan Jingir a Jos

Air Marshal Abubakar, ya ziyarci jihar domin yin ta’aziyya harin bam da rundunar sojin sama ta kai wa wasu mutane bisa kuskure.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta canza matsayarta ba game da ƙin sasanci da miyagun mutane.

“Muna shaida wa kowa cewa ba za mu zauna da ’yan bindiga ba,” in ji shi.

“Hanyar da muka ɗauka tana haifar da sakamako mai kyau, kuma muna ganin zaman lafiya yana samuwa a Zamfara.”

Gwamnan ya kuma yaba da yadda jami’an tsaro ke hanzarin amsa kiran gaggawa a jihar.

“Ina gode wa Hafsan Sojin Sama saboda matakin gaggawa da ya ɗauka. Kafin wannan ziyarar, ya aike da manyan jami’ai domin jajanta mana.

“Wannan yana nuna ƙwazo da jajircewarsu wajen kare lafiyar mutanenmu,” in ji shi.

Hakazalika, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ana gina sabon filin jirgin sama a Zamfara, kuma ya buƙaci a gina wajen ajiye jiragen rundunar sojin sama a ciki don ɗaukar matakan gaggawa kan matsalolin tsaro.

“Muna gina filin jirgin sama a Zamfara. Da zarar an kammala, muna fatan samun wajen ajiye jiragen sojin sama a cikinsa domin hanzarta ɗaukar matakan tsaro,” a cewarsa.

Air Marshal Hassan Abubakar ya gode wa gwamnan bisa yadda ya fahimci cewar harin da sojin rundunar suka kai ba da gangan ba ne.

Ya bayyana cewa sojojin sun kai hari ne bisa bayanan sirri kan ayyukan ’yan bindiga, amma daga baya aka gano cewa wasu ’yan sa-kai sun rasa rayukansu a dalilin harin.

Ya tabbatar wa mutanen Zamfara cewa rundunar sojin sama za ta ci gaba da inganta ayyukanta domin kauce wa irin wannan kuskure a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamna Lawal Sakamako Mai Kyau Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Ayukkan Sojoji Na Taimakawa Wajen Samar da Tsaro a Taraba

Kwamandan runduna ta 6 ta sojan Nijeriya a jihar Taraba, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya karbi bakuncin mahalarta kwas din Cibiyar Bayar da Agaji ta Sojojin Najeriya (NARC) karo na 7/2025 a wani rangadin karatu a jihar Taraba a hedkwatar rundunar dake Jalingo.

 

A yayin ziyarar, Janar Uwa ya yi wa mahalarta taron karin haske kan ayyukan gudanar da aiki, nasarori, kalubale, da hasashen da za a yi a nan gaba, inda ya bayyana muhimman nasarorin da aka samu wajen yaki da rashin tsaro a cikin shekarar da ta gabata.

 

Ya yi nuni da cewa al’amuran satar mutane don neman kudin fansa, fashi da makami, da kuma rikicin kabilanci ya ragu matuka saboda jajircewar sojojin.

 

A wani bangare na bayanin, Janar Uwa ya baje kolin makamai da alburusai da aka kwato daga ayyuka daban-daban da aka samu nasara.

 

Ya yaba da kwazo da jajircewar sojojin, wanda jajircewarsu ya taimaka matuka wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

 

A nasa jawabin, shugaban tawagar, Manjo Janar Dahiru Sanusi, wanda ya wakilci Darakta Janar na NARC, Manjo Janar Garba Ayodeji Wahab murabus, ya bayyana godiya ga kwamandan da jami’ansa bisa kyakkyawar tarba da karimcin da suka yi.

 

Ya yi nuni da cewa, an shirya rangadin binciken ne domin fahimtar aiki da kuma aikace-aikace na zahiri, tare da mayar da hankali musamman kan tantance tasirin ayyukan tsaro na rundunar ga kanana da matsakaitan masana’antu (SMEs) a cikin jihar.

 

Za a ci gaba da rangadin ne tare da ziyartan wasu muhimman wurare a fadin jihar ta Taraba, domin baiwa mahalarta damar fahimtar yanayin tsaro da kuma rawar da sojojin Najeriya ke takawa wajen samar da kwanciyar hankali da tsaro.

 

PR/ Sani Sulaiman

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Gwamnatinsa Na Bai Wa Sojoji Haɗin Kai 
  • ’Yan bindiga: Har yanzu Janar Tsiga na tsare bayan kwanaki 29
  • Ayukkan Sojoji Na Taimakawa Wajen Samar da Tsaro a Taraba
  • ECOWAS Za Ta Aika Kwamitin Sulhu Zuwa Ƙasashen AES
  • PDP Ta Caccaki Gwamnan Gombe Saboda Rabon Tallafin Abinci….
  • An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai
  • Matashi ya hallaka mahaifiyarsa da duka a Bauchi
  • Ana zargin wata mata da kashe kishiyarta a Bauchi
  • Wata mata ta kashe kishiyarta a Bauchi