Aminiya:
2025-04-07@19:36:04 GMT

’Yan bindiga: Har yanzu Janar Tsiga na tsare bayan kwanaki 29

Published: 6th, March 2025 GMT

Kwanaki 29 ke nan da wasu ‘yan bindiga suka mamaye garin Tsiga da ke ƙaramar hukumar Bakori a Jihar Katsina, inda suka yi awon gaba da Birgediya Janar Maharazu Tsiga mai ritaya da wasu mutane.

An yi garkuwa da Tsiga, wanda tsohon Darakta-Janar na Hukumar Yi Wa ƙasa hidima (NYSC) ne tare da wasu mazauna garin su tara, a wata ranar Laraba.

An kama ’yan Pakistan biyu da laifin yin garkuwa a Legas Hukumar Zaɓen Neja ta sanar da ranar zaɓen ƙananan hukumomoni

Masu garkuwa da mutanen sun tuntuɓi iyalan Janar ɗin da aka sace domin neman kuɗin fansa na Naira miliyan 250m.

Wata majiya ta kusa da dangin ta shaida wa wakilinmu cewa, har yanzu ana ci gaba da tattaunawa da nufin ceto Janar ɗin sojan mai ritaya.

“Abin takaici ne yadda har yanzu Janar ɗin da sauran waɗanda suka yi garkuwa da su suna hannun waɗanda suka sace su a cikin wannan wata na Ramadan.

“Zan iya tabbatar muku da cewa ana tattaunawa, kuma addu’o’inmu na tare da shi da duk sauran waɗanda abin ya shafa da ke tsare,” in ji majiyar.

Wata majiyar kuma na kusa da dangin, ta bayyana fargabar yin magana da manema labarai, inda ta ce bisa ga bayanan da aka yi ta yaɗa jita-jita game da sace Janar ɗin, zai yi musu wuya su ce komai ga ‘yan jarida.

Sai dai ya tabbatar da wata majiya na cewa ana ci gaba da tattaunawa don ganin an sako Janar ɗin.

A halin da ake ciki, rundunar ’yan sanda a Jihar Katsina ta ce, ana ci gaba da ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar tarayya da ke Dutsin-Ma da aka sace.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiƙ Aliyu, ya ce rundunar ’yan sandan tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro na ƙoƙarin kuɓutar da wandanda aka sace tare da kamo masu laifin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Janar Tsiga

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025

Gwamnan ya taya al’ummar Musulmi murna bisa kammala azumin watan Ramadan tare da addu’ar Allah ya karvi ibadu.

“Ina addu’ar Allah ya ci gaba da ba mu zaman lafiya da kwanciyar hankali tare da hadin kai a tsakani. Za mu ci gaba da shaidar bukukuwan Sallar.

“Ina kuma gode wa shugabannn addininmu bisa koyar da mu alkur’ani mai girma. Ina fatan wasu shekarun za su samemu cikin kwanciyar hankali,” Sanwo-Olu ya shaida.

Ita kuma a nata vangaren, matar gwamnan jihar, Dakta Ibijoke Sanwo-Olu, ta nuna farin cikinta kan yadda ake gudanar da shagulan salla a jihar cikin kwanciyar hankali tare da yin kira ga mutanen Legas da su ci gaba da nuna soyayya da kauna ga wadanda ba su da karfi da marasa galihu ta hanyar musu kyautuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rahoto: Yara Falasdinawa 350 ne Isra’ila ke tsare da su a gidajen kurkuku
  • Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba
  • ’Yan sanda sun janye gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Tasirin Shirin NYSC Bayan Shekaru 50 Da Kafa Shi?
  • ’Yan sanda sun soke gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga a Taraba
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
  • An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe
  • An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe