Jamhuriyar Musulinci ta Iran ta yi watsi da zarge-zargen da jami’an Birtaniya suka yi na cewa Tehran na barazana ga tsaron kasar ta Burtaniya.

A cewar jami’an Iran, Ingila na zargin Iran da wani abu da ta yi fice a kai.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghai, ya mayar da martani da kakkausan lafazi kan wannan zargi, yana mai cewa wannan maganar banza ce.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafin X, ya tunatar da cewa ita kanta kasar Birtaniya kwarariya ce wajen tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe.

A kwanakin baya ne sakataren tsaron Burtaniya Dan Jarvis ya gabatar da shawarar a gaban majalisar dokokin kasar cewa za a kara sa ido kan gwamnatin Iran da suka hada da jami’an tsaronta da kuma dakarun kare juyin juya halin Musulunci a karkashin wani sabon tsari don dakile barazanar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 2 Sun Yi Shahada A Wani Hari Da Jirgin Sama Maras Matuki Na HKI Ya Kai Wa Kasar Lebanon

Rahotanni da suke fitowa daga yankin ‘Sahalul-Khayam na kasar Lebanon sun ce, wasu ‘yan asalin kasar Syria su 2 sun yi shahada sanadiyyar harin da Isra’ila ta kai da jirgin sama maras matuki sa’o’i 2 da su ka wuce.

Da safiyar yau Litinin ma dai wani karamin jirigin ‘yan sahayoniya ya jefa bom akan wata mota da take tafiya a garin “Beit-Lif” a kudancin kasar da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar wanda ke cikinta.

Hare-haren da HKI take kai wa a kudancin Lebanon din dai yana a karkashin keta hurumin kasar da kuma kin aiki da kudurin MDD mail amba 1701 na tsagaita wutar yakin da aka yi a ranar 27 ga watan Nuwamba na wannan shekara ta 2025.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Amruka Tana Mafarkin Kulla Yarjejeniya Da Iran Kwatankwanci Wacce Ta Yi Da Kasar Libya
  • Mutane 2 Sun Yi Shahada A Wani Hari Da Jirgin Sama Maras Matuki Na HKI Ya Kai Wa Kasar Lebanon
  • Matakin Sin Na Karfafa Takaita Fitar Da Abubuwa Masu Alaka Da Ma’adanan “Rare Rarth” Na Nuni Ga Aniyarta Ta Kare Tsaron Kasa
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Araqchi: Iran ba ta da matsala game da tattaunawa amma ba za ta lamunci yi mata barazana ba
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Pezeshkian ya soki barazanar Amurka kan kasarsa game da tattaunawar nukiliya
  • Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Amurka Da Jakadan Sin A Burtaniya Sun Nuna Adawa Da Matakin Harajin Fito Na Ramuwar Gayya Da Amurka Ta Dauka
  • Pezeshkian: Iran ba ta neman yaki da kowace kasa
  • Wani Kusa A Kungiyar Hamas Ya Yi Shahada A Wani Harin Isra’ila A Kudancin Lebanon