An Ayyana Dokar Ta-baci A Wasu Yankunan Siriya
Published: 7th, March 2025 GMT
Gwamnatin Syria ta ayyana dokar ta-baci a yankuna da dama na kasar bayan da aka gudanar da zanga-zangar nuna adawa da yadda gwamnatin kasar ke kara murkushe fararen hula.
An sanya dokar ta-baci a birnin Tartus da ke arewa maso yammacin kasar da kuma daukacin lardin Homs a daren Alhamis.
An kuma sanar da dokar hana fita a Latakia har zuwa karfe 10:00 na safe agogon kasar ranar Juma’a.
Dokar hana fita ta biyo bayan zanga-zangar da ‘yan Alawiyyawa da mabiya Shi’a suka yi, wadanda suka yi Allah wadai da ta’addancin gwamnatin.
Sun zargi gwamnatin rikon kwarya ta Syria da fifita mulki kan sake gina al’ummar kasar.
Majalisar koli ta addinin musulunci ta Alawite a kasar Syria ta fitar da wata sanarwa, inda ta yi tir da karuwar tashe-tashen hankulan da gwamnatin kasar ke yi, da suka hada da kai hare-hare ta sama kan gidajen fararen hula da tilastawa mazauna su kauracewa gidajensu.
Sanarwar ta yi kira ga al’ummar Syria da su gudanar da zaman lumana tare da kauracewa barnatar da dukiya ko kuma shiga rikicin kabilanci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojonin Yemen Ta Kakkabo Jiragen Yakin Amurka Wadanda Kimarsu Ya Dalar Amurka Miliyon $200 A Makonni 6
Sojojin kasar ayemen sun kakkabo jiragen yaki na kasar Amurka wadanda ake sarrafashi daga nesa a kan kasar Yemen, da dama wadanda kimarsu ya kai dalar Amurka miliyon $200 a cikin makonni 6 kacal.
Tashar talabijin ta Pressstv a nan Tehran ya bayyana cewa wadan nan jiragi suna aikin leken asiri ne a kan kasar ta Yemen, kuma duk da cewa suka tashi fiye da kafa 40,000 a sama, amma sojojin yemen suna iya kakkabosu.
Wannan yana zuwa ne a dai lokacinda shugaban kasar Amurka Donar Trump ya kara umurnin a kara yawan hare-haren da ake kaiwa kasar ta Yamen.
Mafi yawan hare-haren da suke kaiwa yana kasa mata da yara da kumalalata kamfanoni da kuma cibiyoyin samar da ruwa ko ajiyar makamashi ne .
Don haka hare-haren basa kaiwa ga makaman sojojin kasar Yemen wadanda suke karkashin kasa kuma nesa daga inda makaman Amurkka zasu samesu.
Amurka dai ta fara yake da Yemen ne don tallafawa HKI kan hare –haren sojojin yemen kanta tun baya sake dawoda yakin dofan al-aksa.