HausaTv:
2025-04-27@19:41:12 GMT

Hamas Ta Ce A Shirye Take Kan Komi, Kan Barazanar Trump

Published: 7th, March 2025 GMT

Bangaren soja na kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ya ce a shirye yake kan komi ma, kuma zai ci gaba da kasancewa cikin “kyakyawan shiri”, yana mai jaddada cewa barazanar da Isra’ila ke yi na sake yaki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya ba zai sa a sako Isra’ilawan da aka yi garkuwa da su ba.

Abu Ubaida, kakakin kungiyar al-Qassam Brigades, ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya yi a faifan bidiyo a ranar Alhamis, yana mai jaddada cewa, abin da ‘yan mamaya suka kasa cimma ta hanyar “makamai da yaki” ba za a taba samun shi ba ta hanyar “barazana da yaudara ba.”

Kalaman nasa sun zo ne kwana guda bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar cewa za a kashe Falasdinawa a zirin Gaza da mayakan Hamas matukar ba’a gaggauta sako sauran Isra’ilawan da ke hannun Hamas ba.

Shugaba Trump ya bukaci Hamas ta gaggauta sakin dukkan mutanen da take garkuwa da su a Gaza – inda ya yi barazanar cewa za ta dandana kudarta idan har ba ta saki sauran mutanen ba.

Ya kuma yi kira ga Hamas ta fice daga yankunan Falasdinawa tare da yin gargadi ga al’ummar Gaza cewa za su fuskanci mutuwa idan har ba a saki mutanen da Hamas ke tsare da su ba.

Trump ya yi gargadin ne ga Hamas a sakon da ya wallafa a kafarsa ta sada zumunta inda ya ce zai sa Isra’ila ta kammala aikin da ta soma wajen kakkabe Hamas.

Gargadin na Trump na zuwa ne yayin da Fadar White House ta tabbatar da cewa tana tattaunawa da Hamas domin sakin mutanen da kungiyar ke tsare da su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasarsa A Shirye Take Ta Sulhunta Tsakanin Pakistan Da Indiya

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Iran a shirye take ta inganta fahimtar juna tsakanin Indiya da Pakistan

Ministan harkokin wajen Iran Sayyid Abbas Araqchi ya sanar a yau Juma’a cewa: kasarsa a shirye take ta yi aiki mai kyau a fagen sulhunta tsakanin Indiya da Pakistan don inganta fahimtar juna tsakanin bangarorin biyu a wannan mawuyacin lokaci.

Da yake tsokaci game da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan tsakanin Indiya da Pakistan, Araqchi ya bayyana cewa: “Indiya da Pakistan kasashe ne ‘yan uwan ​​juna kuma masu makwabta da Iran, kuma suna da alakar al’adu da wayewa tun shekaru aru-aru.”

Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: “Suna daukar kasashen Indiya da Pakistan a matsayin sauran makwabtansu, kuma masu matsayin fifiko na farko.” Don haka Iran a shirye take ta yi amfani da dukkanin kwarewarta wajen kyautata alaka tsakanin Pakistan da Indiya, don inganta fahimtar juna a tsakanin bangarorin biyu a cikin wannan lokaci mai wuyar gaske.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falasdinawa 39 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’o’I 24
  • Hamas Ta Yi Allawadai Da Dage Rigar Kariya Na Ma’aikatar Hukumar UNRWA
  • Sojojin Mamaya Sun Yi Kasan Kiyashi A Zirin Gaza Da Kuma Ci Gaba Da Killace Falasdina  Cikin Masifar Yunwa
  • Gaza: Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A  Yau Asabar
  • Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Gargadin Munanan Sakamakon Da Zai Biyo Bayan Kashe Falasdinawa
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Natenyahu Ba Zai Hadi Fada Da Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasarsa A Shirye Take Ta Sulhunta Tsakanin Pakistan Da Indiya
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Faransa ta jaddada aniyarta na ci gaba da tattaunawar nukiliyar iran