Leadership News Hausa:
2025-04-07@20:39:26 GMT

Wajibcin Azumi

Published: 7th, March 2025 GMT

Wajibcin Azumi

 

Jinkirta Sahur Da Gaggauta Buda-baki

An karba daga Anas, ya ce, Annabi SAW ya ce “ku dinga yin Sahur, domin shi yin Sahur akwai albarka a cikinsa”, ba burgewa ba ce mutum ya dinga cewa ‘ai ni ban yin sahur’ albarka mai yawa ta wuce shi.

An karba daga Sahlu dan Sa’adu Allah ya kara yarda da shi ya ce, Manzon Allah (SAW) ya ce “Mutane ba za su gushe ba cikin alkairi muddin sun gaggauta yin buda-baki” Ma’anar wannan hadisi, sabida Allah ya fada cikin Alkur’ani “summa atimmus siyama ilallai – sannan ku cika azumi zuwa dare” sai Annabi ya koya mana sunnarshi zuwa dai-dai lokacin da ya dace na buda-bakin (ba cikin dare Allah yake nufi ba), sai Annabi SAW ya bayyana da fadarsa ku gaggauta yin buda baki – da rana ta fadi, an sha ruwa.

Manzon Allah (SAW) ya kasance in an sha ruwa yana fara bude baki ne da addu’a inda yake cewa “Allahumma laka sumtu wa ala rizkika afdartu – Ya Allah a gareka nake Azumi kuma cikin arzikinka nake buda-baki” mai azumi cikin hadarar Allah yake don haka a wurin mai arziki mai azumi yake shan ruwa.

An karba daga Abi Zaidil Gifari ya daga hadisin zuwa ga Annabi SAW yace “Ma zala Ummati bi khairin ma anta … – Al’ummata ba za ta gushe ba tana cikin alkairi matukar tana yin buda-baki sannan kuma ta jinkirta sahur”. Shi buda-baki ana son gaggautawa, sahur kuma ana son jinkirtawa zuwa karshen dare.

An karba daga Abdullahi bin Maz’unu yana cewa Sahabban Manzon Allah (SAW) sun kasance mafi gaggawar mutane buda-baki sannan mafi jinkirin mutane sahur. Baihaki ne ya ruwaito hadisin da sanadinsa ingantacce.

Abu Dawud ya ce, Abu Abdullahi ya ce “Idan Mutum ya yi kokonto cikin alfijir to ya yi ta cin abincinsa har sai ya sakankance alfijir ya futo.” Wannan ita ce nasabar Abdullahi bin Abbas da Adda’u da Auza’i da Ahmadu bin Hambali.

An karba daga Anas Allah ya kara yarda da shi ya ce “Manzon SAW ya kasance yana buda-baki da danyen dabino, in ba a samu danye ba sai ya yi da busassshe idan ba a samu ba sai ya sha ruwa kadan”. Abi Dawud da Tirmizi suka ruwaito Hadisin. Addinin Musulunci balaraben addini ne, dabino yana daga cikin alamun addinin musulunci don haka ya dace gwamnati ta kula da sana’ar dabino musammam lokacin azumin watan Ramadan. Sabida wannan dabinon da muke buda baki da shi, ba musan shekararsa nawa da yanko shi kasa ba.

Amma akwai wata hikima da ake yi wajen maida busassshen dabino zuwa danyen dabino. Da safe, sai mutum ya dibo iya wanda zai yi buda baki da shi, ya wanke dabinon, sai ya nemo ruwan zafi, ya jika a ciki sai ya kulle robar da ya jika dabinon zuwa lokacin buda-bakin.

 

Kiyaye harshe daga alfasha

An karba daga Abi Huraira Allah ya kara yarda da shi, shi kuma ya karba daga Manzon Allah (SAW) ya ce “Azumi ba wai barin ci da sha ne kawai azumi ba, azumi barin maganar batsa da maganar da ba ta dace ba, idan wani ya zage ka ko ya dame ka, to ka ce masa ni ina azumi”, Hakim ya ce ingataccen hadisi ne.

“Manzon Allah (SAW) ya ce duk wanda bai bar gulma da kagen karya da kitsa sharri ba a azumi, Allah ba shi da wata bukata da azuminsa.”

Ya zo daga Annabi (SAW) yana cewa “da yawa wasu ba su da Ladan azumi sai dai wahalar kishirwa da shan yunwa kawai, da yawa mutum ke sallar dare amma ba su da ladan sallar sai dai wahalar tsayuwa kawai.” Hadisin Ingatacce ne abisa sharadin Bukhari.

 

Yin aswaki da azumi abu ne mai kyau

Asiwaki da kyauta da yawaita karatun Alkur’ani da yawaita ibadu a cikin watan Ramadan duk Allah yana son hakan musamman a goman karshe ta watan.

Ya zo a cikin ingatattun hadisai daga Amiru yana cewa “da yawa na ga Annabi (SAW) ba daya ba biyu ba kai ba za su kidayu ba yana yin asiwaki kuma yana cikin azumi.”

Sayyada A’isha uwar Muminai ita kuma ta saukaka ta ce mutum zai iya sa abun kamshin baki a bakinsa, don bakin ya zama ba ya wari ya yi kamshi, sabida su Larabawa al’adarsu suna sumba, sharadi dai kar ya shiga makogoro. Wannan ijtihadi ne na Sayyada A’isha. Mace mai girki ta iya dandanar gishiri sai ta tofar ko mai sana’a irin wacce sai an dandana ake gane ingancin sana’ar, za su iya dandanawa sai su zubar. Haka mai alwala, in ya tofar da ruwan bakinsa sau uku, abin da ya biyo baya ba ruwa ba ne, miyau ne.

Bukhari ya ruwaito daga Abdullahi bin Abbas cewa Manzon Allah (SAW) shi ne mafi kyautar mutane amma babban lokacin kyautar Manzon Allah (SAW) ita ce Ramadan, lokacin da Mala’ika Jibrilu ke zuwa su yi musaffar Alkur’ani.

Duk abin da Mala’ikah Jibrilu ya zo wa Annabi da shi a wannan shekara, to sai sun yi musaffar wannan karatun a watan Ramadan. Sabida haka ne Annabi (SAW) yake ninka kyautarsa a watan Ramadan.

An ruwaito daga Sayyada A’isha ta ce Annabi (SAW) idan goman karshen watan Ramadan ta shigo yana raya daren duka.

Mai azumi zai iya shiga Shawa ya yi wanka, zai iya shiga kogi matukar ruwa ba zai shiga cikinsa ba, mai azumi zai iya zuba ruwa a kansa don ya ji sauki, kuma zai iya kuskure bakinsa. Ba laifi don an yi kiran sallar fitowar alfijir, mutum ya yi wankan Janaba. Wanda ya yi mafarkin saduwar aure da rana a watan azumi bai bata masa azumi ba,. Wanda ruwa ya kubuce masa lokacin alwala, azuminsa bai lalace ba, amma zai rama daya bayan Ramadan. Kurar kan hanya ba za ta bata wa mutum azumi ba, duk abin kasuwancin da sai an dandana ake gane ingancinshi, dandanawar ba za ta karya azumin ba.

Abin da ke karya azumi sun hada da: janyo amai da gangan, zuwan haila, zuwan haihuwa, janyo maniyyi da gangan, ci ko sha daga fitowar alfijir zuwa faduwar rana, saduwa da iyali daga futowar alfijir zuwa faduwar Rana.

Mutum wanda zai ba da zakkar buda-kai zai iya yin ta yanzun (farkon azumi) ya bai wa talakan da bai da dama don ya samu abun buda-baki da shan ruwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 103

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suak zo cikin al-kur’ani  mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawi na m,aulana Jalaluddin Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatana masu sauraro zasu kasance tare da mu.

///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan lamami na biyu daga limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (s) diyar manzon All..(s).

A cikin shirimmu da ya gabata mun ji yadda Khalifa na biyu, a lokacinda ya zo mtuwa ya kafa shura na mutane 6 wadanda yace dukkaninsu manzon All…(s) ya yardadasu kafin ya bar duniya sannan ya bukaci su zabi daya daga cikinsu a matsayin khalifa a bayansa. Mun bayyana cewa ya sanya Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a) daya daga cikinsu amma ya tabbatar da cewa ba zasu taba zabensa a matsayin Khalifa ba, saboda dalilain da ya kawo, na shugabantar da Abdurrahman dan Auf, wanda ya kasance surukin Uthman Dan Affan, sannan Sa’adu dan Abiwakkasa ba zai sabawa dan amminsa Abdurrahman dan Auf ba, Sannan dama Aliyu (a) baya shiri da Talha dan ubaidullah wanda ya nuna cewa a yawa Uthman zai fishi idan an raba biyu ma Abdurrahman dan Auf baya tare da shi.

Sannan munji yadda Khalifan ya aibatasu gaba daya, daga cikin har’da Amurul muminina (a) inda ya zargeshi da wargi da wasa, amma ya tabbatar da cewa idan da zasu bashi ita da ya kaisu kan hanya madaidaiciya, da kuma ya kaisu kan gaskiya.

Kafin haka yace da Salim maula Abu khuzaifa yana nan da ya nada shi Khalifa, sannan da Abu Ubaida dan jarrah yana nan da ya nadasu a matsayin Khalifa kai tsaye.

Idan muka koma baya zamu ga yadda wadannan mutane biyu suke tare da su a ranar wafatin manzon All…(s) da kuma rawan da suka taka wajen tabbatar da cewa Khalifanci ta fita daga hannun Amirul mumimina (s) ta kuma koma hannun Khalifa na farko.

Amma a cikin shirimmu na yau zamu ga yadda aka gudanar da Zaben khalifa a tsakanin mutane 6 wadanda Khalifa na biyu ya bada umurnin su zabi guda daga cikinsu.

Da farkon dangane da cancantar Amirul muminina da Khalifanci, Khalifa Umar bai fi manzon All..(s) sanin haka ba, don a aikace ya nada shi a Ghadir, sannan a lokacinda ya nada shi yace ‘wanda na kasance shugabansa to Aliyu wannan shugabansa ne” yace Ubangiji ka jibanci wanda ya jibance shi ka kuma tabar da wanda ya tabar da shi, ka kuma risker da gaskiya a gareshi a duk inda ya juya.  A wani hadisi, ya ce: Da zasu dora Aliyu da zasu sameshi shiryeyye mai shiryatarwa.

Malamai da dama sun bayyana ra’ayinsu dangane da shuraa ta Umar, kuma sun wadannan al-amura, daga ciki.

01-Ya shirya shura ne kawai don kauda Aliyu (a) daga Khalifanci, saboda ya sanya mafi rinjayen mambobin shoran makiyan Aliyu dan Abitalib (a) wadanda suka hada banu Umayya da Banu Taim. Wato dangin Khalifa na farko. Talha dan ammin Abubakar ne, banu taim, wanda yake adawa da Aliyu dan Abitalib (a). Saboda husuma da yayi da dan amminsa bayan wafatin manzon All..(s) dangane da Khalifanci. Da Uthman da Abdurrahman dan Auf, dangin Banu umayya ne wadanda suke ganin Aliyu ya kashe shuwagabannin su a manya-manyan yake-yaken da aka yi a farkon musulunci. Wato a yakin Badar da Uhudu, da Ahzab da.

Don a lokacinda Aliyu ya karmi khalifanci, Abdurrahman dan Auf ya na daga cikin wadanda suka ki yi masa bai’a bayanda mutane suka zabe shi, Aliyu bai tilasta masa ba.

2-Aliyu dan Abitaliba ya na daukar Zubair dan Awwam, a matsayin shi’arsa ne, saboda yana tare da shi a lokacinda aka kwace khalifanci daga wajensa bayan wafatin manzon All…(s). Zubair ya na gidansa sanda Umar da wasu sahabban suka shiga gidansa suka fitar da shi masallaci don yin bai’a.   

Don haka atakaice, Umar ya nufi ya kawar da Khalifanci daga Aliyu dan Abitalib (a) a wannan karon ma.

Sannan wani abin mamaka da shura, shi ne, Khalifa ya ce manzon All..(s) ya rasu yana mai yarda da wadan nan mutane 6, amma kuma yace idan sun wuce kwanaki uku basu zabi wani daga cikinsu ba, aka kashe su. Zababbun kuma wadanda manzon All…(s) ya yi wafati yana mai yarda da su ne za’a kashe? Abin mamaki.

Sannan yace: idan sun rabu gida biyu mutane uku uku, bangaren da Abdurrahman dan Auf yake ne zai zama mai rinjaye. Kamar babu Aliyu dan Abitalib (a) a cikinsu, ta yaya zai gwatanta Abdurraman dan Auf da Amirul muminina (a).? wanda Imam Ali (a) ya halaka danginsa kafirai da dama a yake-yaken badar da Uhud da sauransu.

Sai kuma taron zaben Khalifa, wanda wasu suka ce an yi shi ne Baitul Mali na lokacin a birnin Madina. Wasu kuma suka ce an yi shi a gidan wani mutum wanda ake kira. Musawwar dan Mukhrimah.

Sannan Imam Hassan (s) jikan manzon All..(s) ya halarci wannan taron na zaben khalifa, hakama Abdullahi dan Abbas ( r) , sannan Amru dan Asi da Mughirah dan shiab sun zo kusa da inda ake zabe,  a daya daga cikin wuraren nan biyu da muka ambata. Sannan yansanda jami’an tsaro na lokacin suka yiwa wurin kawanya, don tabbatar da cewa an aiwatar da wasiyyar Umar,

Don haka mutanen 6 suka zo kusa, sai Imam Aliyu dan Abitalib,(a) ne ya fara tashi, daga cikinsu ya yiwa mutanen nan 5 wa’azi ya gargade su, yace masu su ji tsoron All..su mayar masa da hakkinsa, wanda All..Ta’ala ya nada shi, manzon All..(s) ya kuma zartar da nadin, a wurare da dama a rayuwarsa.

Da ga karshen ya ja kunnensu kan cewa idan basu na da shi ba, to kuwa zasu ga abinda ba sa so a cikin al-ummar musulmi, zasu rarraba, sannan za’a sami wadanda zasu zubar da jinni musulmi don neman wannan kujerar ta Khalifanci ba tare da suna da hali guda mai kyau daya da ya bashi damar zama Khalifa ba.

Da ba’a zabeshi daga karshe ba, mun ga yadda Mu’awiya dan Abisufyan, wanda bai musulunta bas ai shekaru biyu kafin wafatin manzon All..(s) ya zo yana jayayya da Aliyu dan Abitalib (a), wanda shi ne farkon musulunta, sannan shine jarumin dukkan manya-manyan yake yake a musulunci, kamar Badar da Uhudu da Ahzab. Yana jayayya da shi kan khalifancin manzon All..(s). kuma sai da ya zama, tare da taimakon wasu manufurai, ba ma kawai shi ba, sai da yayansa da jikokinsa suka yi Mulki na shekaru fiye da 100 a bayansa a matsayin Khalifofin manzon All..(s).

Suka yiwa musulunci da musulmi barnan da ba’a taba gyaransa ba har duniya ta nade.

Sun yaki yayan manzon All..Tsarkaka sun koresu a bayan kasa, suka bisu a ko ina suka je a duniya suka kakkacesu. Don haka abinda Imam Ali(a) ya fada masu a taron zaben khalifa bayan mutuwar Umar duk sun faru.

A cikin littafin Tarikhin umammu wal-muluk ya kawo bangare na Khudubar Imam Ali a lokacin zaman zaben khalif ana ukku. Inda yake cewa:

{..ba wani wanda ya rika ni amsa kira zuwa gaskiya, da sada zumunci,..har zuwa inda yake cewa…ku saurari zance na, ku fahinci manufata, -idan baki yi abinda ya dace ba to kuma –da sannu zaku ga wannan al-amari (wato Khalifanci) ana zare takubba don nemansa, sannan a karya alkawulla da don nemansa, sai yak aiga wasu daga cikinsku sun zamo shuwagabannin bata, kuma magoya bayan mutanen jahiliyya} kamar yaddayazo cikin littafin sharhin Nahjul Balagh ana sheikh Muhammad Abduh..

Da masu shura sun ajiye son zuciyarsu gefe, sun dubi maslahar musulunci, suka mayarwa mai  hakki hakkinsa, da dukkan wadannan musibu basu sami al-ummar musulmi ba.

Don haka an yi ta ja yayya tsakanin wadanan mutane 6, a rana ta farko, sun kasa zaben day daga cikinsu, an sake yin taro a rana ta biyu an kasa zaben mutum daya. Kuma wasiyar Umar itace a kashe dukkan mutum shida idan sun kasa zaben daya daga cikinsu bayan kwanaki uku.

A nan sai Abu Talha Al-ansari, ya zo wajensu yana cewa, {Ba zan kara baku ko kwana guda ba, idan wa’adin kwanaki uku ya cika zamu zartar da wasiyyar Khalifa a kanku ne}.

A nan ne sai suka kulla wata zaman, sai Talha dan’ubaidullahi ya tashi yace ya bawa bawa Uthman kuri’arsa, wato ya zabi Uthman, wannan kuma a fili yake, saboda fitattun yan takarar sune Aliyu dan Abitalib (a) da kuma Uthman dan Affan. A nan sai Zubair ya tashi shi ma, sai yace, ya bawa Aliyu dan Abitalib (a) kuri’arsa.

Daga nan sai Sa’ad dan Abiwakkas ya tashi yace, ya bawa Abdurrahman dan Auf kuri’arsa, kada ku manta shi dan amminsa ne.

Sannan Abdurrahman ya ga cewa ba zai iya zama Khalifa a kan wadannan biyu ba, wato Aliyu ko Uthman, don haka sai ya nemi shawarar Kuraishawa, suka ce masa ya zabi Uthman.

A nan Abdurrahman bin Auf shi ne mai raba gardama, idan ya koma gefen Aliyu, (a) , shi ne Khalifa, don a lokacin zasu zama masu kuri’u 4. Aliyu, da Zubair da kuma Abdurrahman dan Auf da kuma Sa’ad dan Abiwakkas.

Idan kuma ya koma gefen Uthman, zasu zama ‘kuri’u 4 shi ma, ga Uthman da Talha, ga kuma Sa’adu da kuma shi Abdurrahman. A nan sai ya zabi komawa ga Uthman, sai Uthman ya zama Khalifa. Aka bar Aliyu (a) da kuri’u biyu.    Masu sauraro a nan zamu dasa aya sai kuma wata fitowaidan All..ya kaimu wassalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sayar da kare mafi tsada a duniya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci
  • Abin da ya sa ba ma cin naman Akuya — Fulani
  • Tsohon Gwamnan Oyo, Omololu Olunloyo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 89
  • Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu
  • Duk Da Matsin Tattalin Arziki, Bukukuwan Sallar Bana Ta Yi Armashi
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 106
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan Ia) 104
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 103