HausaTv:
2025-04-07@20:34:17 GMT

MDD Ta Nuna Damuwarta Da Abinda ke Faruwa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan

Published: 7th, March 2025 GMT

Kakakin babban sakataren MDD ya bayyana damuwarsa kan abubuwan da suke faruwa a yankin yamma da kogin Jordan, inda sojojin HKI suke ci gaba da rusa gidaje, da bata yanyuyi da kuma dukan Faladinawa da suka hadu da su a yankin arewacin yamma da kogin na Jordan.

Tashar talabijin ta Presstva anan Tehran ya nakalto Stephane Dujarric kakakin babban sakataren MDD yana fadar haka a jiya Alhamis, ya kuma kara da cewa, wakilan Majalisar a yankun sun bada rahoton yadda sojojin HKI suka kutsa a cikin sansanin yan gudun hijira na al-Arroub wanda yake cikin yankin Shuyukh al-Arrub, inda suka daki wani matsayi da kasar bindiga har suka fasa masa bakinsa suka kuma karya masa kafa.

Har’ila yau rahoton ya kara da cewa yahudawan sun tilastawa falasdinawa da dama rufe shagunasu da kuma tserewa daga yankin, bayan da suka jefa masu hayaki mai sa hawaye, kuma dauki da guba..Kamfanin dillancin labaran WAFA ta Falasdinawa ya bada irin rahoto guda a yankin. Tun bayan dakarar da yaki a Gaza sojojin yahudawan sun karfafa ayyukan soje a yankin yamma da kogin Jordan da nufin korar Falasdinwa daga yankin kwatakwata

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji

Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji a zirin Gaza, bayan da wasu sabbin hujjojin bidiyo suka nuna yadda sojojin Isra’ila suke harbin motocin daukar marasa lafiya.

Bidiyon da ya ci karo da wani nau’in lamarin da sojojin Isra’ila suka yi cewa “an gano wasu motoci marasa da yawa suna tunkarar sojojin Isra’ila ba tare da fitillu ko alamun motocin ambullance na gaggawa ba”.

Shugaban kungiyar agajin ta Falasdinu Younes al-Khatib, ya bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa kan kashe-kashen, yana mai jaddada cewa ba za a iya amincewa da binciken da sojojin Isra’ila ke jagoranta ba.

“Ba mu amince da duk wani binciken da sojojin suka yi ba, kuma wannan ne ya sa muka fito fili a kan cewa muna bukatar bincike mai zaman kansa kan lamarin,” in ji al-Khatib a wani taron manema labarai a hedkwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York, yayin da yake magana kan harin da ya kashe likitoci da ma’aikatan jin kai 15 a Gaza.

Ya yi Allah wadai da karuwar hare-haren da ake kai wa ma’aikatan jin kai da wuraren aikinsu, yana mai jaddada cewa ana kai hari kan tambarin kungiyar agaji ta Red Crescent, wanda ya kamata a kiyaye a karkashin dokokin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
  •  Kasashen Faransa Masar Da Jordan Sun Yi Taro Akan Gaza
  •  HKI Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Yankin Khan-Yunus
  • ACF ta nemi Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen kisan jama’a a Filato
  • Trump Ya Yada Hutunan Bidiyo Wadanda Suka Nuna Yadda Sojojin Amurka Suka Kashe Mutanen Yemen Wadanda Suke Bukukuwan Salla Karama
  • An Kori Jirgin Ruwan Japan Da Ya Shiga Yankin Ruwan Kasar Sin Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Faifan bidiyo ya fallasa kisan gillar da Isra’ila ta yi wa likitoci  a Gaza
  • Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji
  • Rashin ɗa’a: Gwamnatin Borno ta gargaɗi masu amfani da shafukan sada zumunta
  • Francesca Albanze: Abinda Yake Faruwa A Gaza Kisan Kiyashi Ne