Yansanda A Najeriya Sun Kama Yan Kasar Pakistan Biyu Da Hakanni Wajen Sake Yan Kasashen Waje A Kasar
Published: 7th, March 2025 GMT
Yansanda a birnin Lagos na kudancin kasar sun kama wasu yan kasar Pakistan biyu wadanda suke da hannu dumu-dumi a cikin aikin kamawa don neman kudaden fansa daga hannun wani dan kasar ta Pakistan dan shekara 48 a duniya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran sun nakalto daga kafafen yada labaran kasar wadanda suka ji kakakin yansan na jihar Lagos Chief Superintendent Benjamin Hundeyin yana cewa, yan kasar Pakisatn da suka kama a wani dauki da suka wanda aka sace don neman kudaden fansa sun kama a ranar 5 ga watan maris akwia Roman Gull dan shekara 19 da kuma Aftab Ahmed dan shekarera 28 a duniya kuma yan asalin kasar Pakistan ne, wadanda suka hada kansu da wasu gungun barayi don yin haka.
Ya ce barayin sun nemi dalar Amurka $34,000 ko naira miliyon 50 daga wajensa a matsayin kudaden fansa. Amma kamfanin da yake yiwa aiki sun bada naira miliyon guda kacal a cikin kwanaki uku, inda yan sanda suka shiga suka kuma kubutar da shi. Kuma yansanda suna kokarin gano sauran mutane 5 da suke rage cikin gungun yan fashin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al-Azhar ta yi kira da a kama Netanyahu a matsayin mai laifin yaki
Cibiyar da ke sa ido kan tsattsauran ra’ayi da ke karkashin cibiyar ilimi ta Al-Azhar ta Masar, ta fitar da wata sanarwa da ta yi kira da a kame firaministan Haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu a matsayin mai laifin yaki.
Shafin sawtbeirut.com ya bayar da rahoto kan sanarwar da ke cewa, cibiyar yaki da tsattsauran ra’ayi ta Al-Azhar, ta yi Allah wadai da tarbar da kasar Hungary ta yi wa firaministan Isra’ila, wanda ke fuskantar sammaci na kasa da kasa da kotun ICC ta bayar, ta kuma sanar da cewa: “Manufar wannan mataki shi ne tauye matsayin kotun kasa da kasa da kuma keta hurumin ta.”
Sanarwar ta ce: Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa alama ce ta tabbatar da adalci a duniya, kuma dole ne kasashen duniya su hada kai wajen mara mata baya wajen hukunta masu aikata laifukan yaki.
Kungiyar ta bayyana cewa: shawarwarin kasa da kasa da hukunta wadanda suka aikata laifukan yaki shi ne ginshikin tabbatar da zaman lafiya da adalci, kuma mutane suna da daidaito a gaban doka, babu wani wanda yake a birbishinta.
Sanarwar ta ce: “Babu lokacin yin shiru kana bin da yake fruwa, domin yin shiru yana halasta sabbin laifuka, kuma Gaza ta kasance share fage ne kawai ga ci gaba da aiwatar da bakaken manufofi da zubar da jini, da kashe rayuka.
An fitar da wannan sanarwa ne bayan da kasar Hungary ta yi maraba da firaministan Isra’ila duk da cewa kotun kasa da kasa ta bayar da sammacin kama shi.
A watan Nuwamba 2024, Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta ba da sammacin kama Benjamin Netanyahu bisa zargin aikata laifukan yaki da cin zarafin bil adama a Gaza.
Duk da wannan hukuncin, Netanyahu ya isa kasar Hungary inda ya gana da firaministan kasar Viktor Orban.