Aminiya:
2025-05-06@05:04:21 GMT

Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha

Published: 7th, March 2025 GMT

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, ta bayyana dakatar da ita da Majalisar Dattawa ta yi, a matsayin rashin adalci.

An dakatar da ita ne biyo bayan ta ƙaddamar da ta ɓarke tsakaninta da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan tsarin zama a zauren majalisa a ranar 20 ga watan Fabrairu.

Doyin Okupe: Tsohon kakakin shugaban ƙasa ya rasu Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na watanni 6

Daga baya, ta zargi Akpabio da cin zarafinta, amma ya musanta hakan.

Kwamitin Ladabtarwa da Ɗa’a na majalisar, ya yi watsi da koken nata, inda ya bayyana cewa ba a bi ƙa’ida wajen shigar da ƙorafin ba.

Duk da haka, Natasha ta jaddada cewar ita Sanata ce, kuma za ta ci gaba da wakiltar al’ummarta.

A cikin wani rubutu da ta wallafa a shafukan sada zumunta, ta ce: “Dakatar da ni ba bisa ƙa’ida ba ya saɓa wa adalci da gaskiya.

“Ba zai karɓe min matsayin da ’yan Kogi suka ba ni ba. Zan ci gaba da yi wa mutanena da ƙasata hidima har zuwa 2027—da ma bayan hakan.”

Majalisar ta dakatar da ita na tsawon watanni shida bayan karɓar shawarar kwamitin Ladabtarwa.

Matakin dai ya haifar da zazzafar muhawara s tsakanin ‘yan Najeriya, inda wasu ke ganin an tauye mata haƙƙinta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi dakatarwa zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan California: California Za Ta Ci Gaba Da Bude Kofa Ga Sin Domin Gudanar Da Kasuwanci

Yayin da aka tabo batun manufofin cinikayya da gwamnatin Trump ta dauka, Newsom ya ce, dalilin da ya sa ya soki matakan na gwamnatin Trump shi ne, jihar California ta fi fama da mummunan tasirin da manufofin suka haifar sama da sauran jihohin kasar.

 

Tun bayan da shugaba Trump ya sanar da matakin kakaba haraji a watan Afirilu, Newsom ta yi kira ga kasashe masu karfin tattalin arziki da ke wajen Amurka, da kada su sanya harajin ramuwar gayya kan kayayyakin da ake fitarwa daga jihar California. Kazalika, California ce jihar farko da ta kai karar gwamnatin Trump kan batun harajin. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kano Ta Amince Da Dokar Wutar Lantarki Da Za Ta Raba Wa Jihohi 3 Wuta
  • Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Masifar Yunwa Ta Kara Yin Kamari A Yankin Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Gwamnan California: California Za Ta Ci Gaba Da Bude Kofa Ga Sin Domin Gudanar Da Kasuwanci
  • Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot
  • Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu
  • Amurka Ba Za Ta Cimma Nasara Ta Hanyar Yakin Cinikayya Ba
  •  Syria: A Karon Farkon Jirgi Mai Saukar Angulu Na HKI Ya Sauka A Yankin Suwaidah
  • Har Yanzu Manyan ‘Yan Wasa Suna Son Buga Wasa A Manchester United – Amorim
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Tattauna Da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Kan Zaman Tattaunawan Amurka Da Iran