Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe
Published: 7th, March 2025 GMT
Alkalin kotun ya umarci a kwace kuɗin tare da mika su ga gwamnatin tarayya, bisa tanadin dokar hana safarar kuɗaɗe ta shekarar 2022.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso sun kira jakadunsu daga Aljeriya
Kasashen Mali, Nijar da kuma Burkina faso dake hade a kawancen Sahel na AES, sun sanar da kiran jakadunsu a Aljeriya domin tuntuba.
A wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na kasar Mali a yammacin jiya Lahadi, kasashen uku sun sanar da kirawo jakadunsu domin tuntuba bayan da Aljeriya ta kakkabo wani jirgi marar matuki na kasar Mali a farkon wannan wata.
Aljeriya dai ta kakkabo jirgin sojojin na Mali marar matuki a cikin daren ranar 31 ga Maris zuwa 1 ga Afrilu, matakin da kasashen uku sukayi tir da shi.
A cewar gwamnatin Algiers, jirgin mara matuki da ake magana a kai ya shiga cikin kasar ne, saidai sojojin Mali sun tabbatar da cewa jirgin bai shiga cikin kasar Aljeriya ba.
Lamarin, wanda ya faru mako guda da ya gabata, kaashen na AES a wata sanarwa ta bai daya sun bayyana shi a matsayin “rashin gaskiya” da kuma keta dokokin kasa da kasa.
Firaministan Mali Abdoulaye Maiga ya musanta ikirarin Aljeriya na cewa jirgin mara matuki ya shiga sararin samaniyar Aljeriya, yana mai cewa lamarin ya nuna yadda Aljeriya ke goyon bayan ta’addanci.
A matsayin mayar da martani, Mali ta gayyaci jakadan Aljeriya tare da yanke shawarar janyewa daga kawancen sojan yankin na tsawon shekaru goma sha biyar.
Bidiyon da kungiyoyin ‘yan tawaye suka fitar ya nuna tarkacen jirgin da kamfanin Baykar na Turkiyya ya kera.