Aminiya:
2025-04-11@11:05:22 GMT

Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC

Published: 7th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai na shirin kafa wata sabuwar hukuma da za ta karɓi ikon yin rajistar jam’iyyun siyasa daga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Wannan na zuwa ne bayan da majalisar ta gabatar da wani sabon ƙudiri kan batun.

Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha

Kakakin Majalisar, Hon.

Tajudeen Abbas, tare da Hon. Marcus Onobun daga Jihar Edo ne, suka gabatar da ƙudirin.

Ƙudirin na neman kafa wata hukuma mai zaman kanta da za ta riƙa yi wa jam’iyyu rajista, kula da dokokinsu, da kuma tallafa musu.

Har ila yau, ƙudirin na neman a kafa wata kotu ta musamman da za ta duba ƙorafe-ƙorafen da suka shafi jam’iyyu da rikice-rikicen da ke tasowa a tsakaninsu.

A cewar Hon. Marcus Onobun, wannan matakin ya zama dole domin kawo ƙarshen rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyun siyasa a Najeriya.

A halin yanzu, ƙudirin ya tsallake karatu na biyu a majalisar, lamarin da ke nuni da cewa ana iya ci gaba da duba yiwuwar aiwatar da shi a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jam iyyu Majalisar Wakilai rajista Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Isra’ila ta kashe Falasdinawa 58 a awa 58

Akalla Falasdinawa 58 ne aka kashe tare da jikkata wasu 213 a cikin awa 24 da suka wuce a hare-haren da Isra’ila ta kai a Zirin Gaza.

Ma’aikatar lafiya ta yankin ta sanar cewa wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun makale a karkashin baraguzai da kuma kan tituna, ba za a iya isa gare su ba ta hanyar motocin daukar marasa lafiya da kuma ma’aikatan tsaron farar hula.

Isra’ila ta kashe mutane 1,449 tare da jikkata wasu 3,647 tun bayan da ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta a ranar 18 ga Maris, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Ta kara da cewa yawan Falasdinawa da aka kashe a yakin Isra’ila a Gaza zuwa 50,810, wasu 115,688 kuma sun samu raunuka tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Ya lakada wa ’yarsa duka har lahira Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga Algeria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kafa Dokar Kai Da Komowa A Kudancin Kasar Syria
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa
  • Majalisar Kano Ta Yi Murna Da Lambar Yabo Da Jaridar LEADERSHIP Ta Bai Wa Abba
  • Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — Gwamnati 
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
  • Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum
  • Tsawaita Rajistar Sabunta Shaidar Mallakar Fili: Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Kwace Filaye
  • Yan Sanda A Saudiya Sun Tsare Wata Bafalasdinya Saboda Bayyana Tutar Kasarta A Kan Jakarta A Masallacin Ka’aba
  • Gaza: Isra’ila ta kashe Falasdinawa 58 a awa 58
  • Ya lakada wa ’yarsa duka har lahira