Aminiya:
2025-04-27@16:27:52 GMT

Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti

Published: 7th, March 2025 GMT

Wani mutum mai shekara 52, Salihu Byezhe, ya yanke jiki ya faɗi yayin da ake Sallar Asuba a wani masallaci da ke ƙauyen Gudaba, a Ƙaramar Hukumar Kuje a Babban Birnin Tarayya, kuma daga baya ya rasu a asibiti.

Wani mazaunin yankin, Musa Dantani, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis bayan Byezhe ya yi sahur, ya yi alwala, sannan ya shiga masallaci don yin Sallar Asuba.

Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC NAJERIYA A YAU: Falalar Buɗa-baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi

“Yayin da ake cikin sallah, kwatsam sai ya yanke jiki, nan take wasu daga cikin masu sallah suka riƙe shi suka kuma gaggauta kai shi asibiti.

“Lokacin da suke kan hanyar zuwa asibiti yana numfashi, amma da suka isa, ya rasu,” in ji Dantani.

Likitan a asibitin ya tabbatar da rasuwar Byezhe, inda ya danganta hakan da hawan jini.

Ɗaya daga cikin ’ya’yansa, wanda ke masallaci lokacin da abin ya faru, ya raka su asibiti, kuma ya ce likita tabbatar da rasuwasa.

Daga baya an gano Byezhe yana fama da matsalar hawan jini, wanda ya tashi yayin da ake sallar.

An yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 10:12 na safiyar ranar Alhamis bisa tanadin addinin Musulunci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Jini rasuwa yanke jiki

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi

An garzaya da ita asibitin Misau, daga nan aka mayar da ita zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Azare, inda aka tabbatar da mutuwarta.

Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi, CSP Ahmed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis.

Ya ce waɗanda aka kama sun amsa laifin kuma sun bayyana sunayen wasu da suka haɗa kai da su.

Cikin sauran waɗanda aka kama har da Alkali Kawu, Maule Mai Ride, Mai Tumatir, Danguli, Yakubu da Kura.

Wakil ya ce bincike yana guduna a hedikwatar ‘yansanda ta Misau, kuma sun ƙudiri aniyar ganin adalci ya tabbata.

Ya ƙara da cewa bayan kammala bincike, za a gurfanar da su a gaban kotu domin fuskantar hukunci daidai da laifin da suka aikata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • Sulhu da ’yan bindigar Katsina: Gaba aka ci ko baya?
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
  • Sojojin Mamaya Sun Yi Kasan Kiyashi A Zirin Gaza Da Kuma Ci Gaba Da Killace Falasdina  Cikin Masifar Yunwa
  • An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji
  • An kashe Shugaban coci da wata mace a Benuwe
  • An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano
  • Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
  • ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa 
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi