Aminiya:
2025-04-27@09:51:31 GMT

Najeriya ta kama hanyar gyaruwa – Remi Tinubu

Published: 7th, March 2025 GMT

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta shirya buɗa-baki a Fadar Gwamnati da ke Abuja, inda ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa ƙasar nan na kan hanya gyaruwa nan ba da jimawa ba.

A yayin jawabinta, ta jaddada muhimmancin tausayi da jin-ƙai a tsakanin rayuwar ɗan adam.

Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha

Ta buƙaci kowa ya kasance mai aikata alheri tsakaninsa da Allah, ba don neman yabo ko amincewar mutane ba.

A yayin buɗa-bakin, Farfesa Azeezat Adebayo, Shugabar Sashen Nazarin Addinin Musulunci na Jami’ar Ilorin, ta bayyana cewa tausayi da jin-ƙai su ne ginshiƙai na kyakkyawar rayuwa a tsakanin al’umma.

Ta tunatar da mahalarta buɗa-bakin cewar watan Ramadan lokaci ne na koyon kyawawan ɗabi’u, kuma ana buƙatar a aikata alheri ga kowa, ba wai ga Musulmai kaɗai ba.

Daga cikin manyan baƙi da suka halarci buɗa-bakin akwai Uwargidan Tsohon Shugaban Ƙasa, Dame Patience Jonathan da matar Mataimakin Shugaban Ƙasa.

Sauran sun haɗa da matan gwamnonin jihohi, ministoci mata, matan ministoci da matan shugabannin hukumomin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buɗa baki gyara Najeriya Ramadan shan ruwa Uwargidan Tinubu

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya

Li ya kara da cewa, Sin da Rasha sun bayyana goyon baya ga Iran wajen karfafa tattaunawa da hadin gwiwa da hukumar IAEA. (Mohammed Yahaya)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Kotun Tsarin Mulki Ta Gabon Ta Tabbatar Da Nasarar Nguema A Zaben Shugaban Kasa
  • Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya
  • Muscat Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Kama Hanyar Zuwa Birnin Domin Ci Gaba Da Tattaunawa Da Amurka
  • Muna Farin Ciki Da Karramawar Da Gwamna Abba Ke Samu Saboda Aiki Tukuru – Hon. Ibrahim
  • An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi
  • Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
  • Tinubu Ya Tabbatar Da Aniyar Gwamnatinsa Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani
  • Uwargidan Shugaban Kasar Sin Ta Tattauna Da Takwararta Ta Kasar Kenya
  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu