Najeriya ta kama hanyar gyaruwa – Remi Tinubu
Published: 7th, March 2025 GMT
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta shirya buɗa-baki a Fadar Gwamnati da ke Abuja, inda ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa ƙasar nan na kan hanya gyaruwa nan ba da jimawa ba.
A yayin jawabinta, ta jaddada muhimmancin tausayi da jin-ƙai a tsakanin rayuwar ɗan adam.
Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — NatashaTa buƙaci kowa ya kasance mai aikata alheri tsakaninsa da Allah, ba don neman yabo ko amincewar mutane ba.
A yayin buɗa-bakin, Farfesa Azeezat Adebayo, Shugabar Sashen Nazarin Addinin Musulunci na Jami’ar Ilorin, ta bayyana cewa tausayi da jin-ƙai su ne ginshiƙai na kyakkyawar rayuwa a tsakanin al’umma.
Ta tunatar da mahalarta buɗa-bakin cewar watan Ramadan lokaci ne na koyon kyawawan ɗabi’u, kuma ana buƙatar a aikata alheri ga kowa, ba wai ga Musulmai kaɗai ba.
Daga cikin manyan baƙi da suka halarci buɗa-bakin akwai Uwargidan Tsohon Shugaban Ƙasa, Dame Patience Jonathan da matar Mataimakin Shugaban Ƙasa.
Sauran sun haɗa da matan gwamnonin jihohi, ministoci mata, matan ministoci da matan shugabannin hukumomin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Buɗa baki gyara Najeriya Ramadan shan ruwa Uwargidan Tinubu
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya
Li ya kara da cewa, Sin da Rasha sun bayyana goyon baya ga Iran wajen karfafa tattaunawa da hadin gwiwa da hukumar IAEA. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp