An Bude Cibiyoyin Ciyar Da Masu Azumi A Dan Modi Na Garin Kafin Hausa
Published: 7th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta yi kira ga masu dafa abincin buda baki a karamar hukumar Kafin Hausa da su kasance masu gaskiya da adalci wajen ciyar da masu azumi a wannan watan na Ramadan.
Mai bai wa Gwamna Umar Namadi shawara kan ayyuka na musamman, Alhaji Abdulkadir Bala T.O yayi wannan kiran yayin da yake duba cibiyoyin ciyar da masu azumi na Dan Modi a cikin garin Kafin Hausa.
Alhaji Abdulkadir Bala T.O ya yaba da kokarin wasu daga cikin masu dafa abincin, yayin da ya nuna rashin jin daɗi kan yadda wasu suka karya yarjejeniyar da aka gindaya masu.
A nasa jawabin, Shugaban karamar hukumar Kafin Hausa, Alhaji Abdullahi Sa’idu Nalayi, ya tabbatar da cewar, Karamar hukumar za ta ba da dukkan goyon bayan da ya dace don gudanar da shirin cikin nasara.
Shima a jawabin sa na godiyan masu dafa abincin, Abba Darakta Kafin Hausa ya yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa kaddamar da shirin ciyar da masu azumi.
Ya kuma yi alkawarin ci gaba da kasancewa masu gaskiya da adalci don cimma manufofin da aka sanya a gaba.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina
’Yan bindiga sun kai hari garin Mahuta da ke Ƙaramar Hukumar Kafur a Jihar Katsina, inda suka harbi wani alkali, Rabiu Mahuta, a hannu da kuma dansa.
A lokacin harin na daren Talata, maharan sun raunata mutane uku tare da yin garkuwa da wasu mutane 13, ciki har da matar alƙalin da kuma biyar daga cikin ’ya’ansa.
Wani mazaunin garin da ya zanta ya ce ’yan bindigar sun isa wurin ne da misalin karfe 11:30 na dare, kuma kai tsaye suka nufi gidan alkalin, inda suka kwashe kusan awa guda suna ƙoƙarin karya ƙofar gidan.
Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin NejaDuk da kiran da alƙalin ya yi wa DPO na yankin domin neman taimako, jami’an tsaro ba su iso a kan lokaci ba.
Ya ce, “Da suka samu nasarar shiga gidan, nan take sun harbe shi a hannu, sai ya faɗi a ƙasa. An kuma raunata ɗansa da raunin harbi a goshinsa.”
Wani makwabcinsa, wanda kuma mamba ne a hukumar tsaron al’umma ta jihar da ya yi ƙoƙarin kai ɗauki a lokacin harin, shi ma an harbe shi kuma yana karɓar magani a wani asibiti a Katsina a halin yanzu.
Maharan sun kuma yi garkuwa da wasu mutane biyar a gidan wani mai suna Shehu Maishayi, tare da Malam Sufi Nahi da kuma matar Malam Abdurrazak, wanda ke zaune a wajen garin Mahuta.
Majiyoyi sun ce sojoji sun iso ne kawai bayan da ’yan bindigar suka tsere daga wurin.